"Na Fi Karfinku," Ministan Tinubu Ya Kara Ta da Hazo, Ya Yiwa Wasu Gwamnoni Shaguɓe

"Na Fi Karfinku," Ministan Tinubu Ya Kara Ta da Hazo, Ya Yiwa Wasu Gwamnoni Shaguɓe

  • Nyesom Wike ya ƙalubalanci dukkan waɗanda ke ganin suna faɗa da shi, ya ce ko sun haɗa kai ba za su taba cin nasara a kansa ba
  • Ministan babban birnin tarayya ya kuma waiwayi gwamnonin PDP, inda ya ce tun farko ya gargaɗe su kar su sa hannu a rigimar siyasar Ribas
  • Wike ya yi wannan furucin ne a wurin liyafar da ƴan kabilar Ijaw suka shirya masa a Fatakwal ranar Asabar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rivers - Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ƙara rikirkita jam'iyyar PDP kan rikicin siyasar da har yanzu ya ƙi ƙarewa a jihar Ribas.

Wike ya bayyana cewa ya fi ƙarfin duk wanda zai shiga takun saƙa ko ya yake shi, yana mai cewa dukkan masu adawa da shi ba za su iya cin galaba a kansa ba.

Kara karanta wannan

"Wa ka taba ginawa": Tsohon gwamna ga yaronsa gwamnan PDP, ya bugi kirji

Nyesom Wike da Gwamna Fubara.
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya kalubalancin dukkan masu takun saka da shi a rikicin siyasar Rivers Hoto: Nyesom Wike, Sir Siminalayi Fubara
Asali: Facebook

Ministan ya kuma musanta raɗe-raɗin ƴan ƙabilar Ijawa sun juya masa baya a rikicinsa da Gwamna Siminalayi Fubara, wanda ya fito daga kabilar, Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Nyesom Wike ya yi wannan furuci ne a wurin liyafar da ƴan ƙabilar Ijawa suka shirya domin karrama shi a Fatakwal, babban birnin Ribas jiya Asabar.

Ministan Abuja ya musanta raba gari da Ijaw

Mista Wike ya ce ya zabi ya maida Fubara magajinsa duk da hakan ya saɓawa ra'ayin wasu 'yan kabilar Ijaw a zaɓen 2023.

“Ba gaskiya ba ne cewa mutanen Ijaw suna fada da ni, uba na iya haifar 'ya'ya 12, ɗaya ya zama zakka ya zama ɗan fashi.
"Mutanen da ke shiga gidan talabijin suna zagi na, ina suke lokacin da muka maida ɗan Ijaw ya zama gwamna?"
"Babu wanda ke faɗa da ni, na fi karfin a sa ƙafar wando ɗaya da ni, duk waɗannan mutanen da kuke gani idan suka haɗa kai ba za su iya ja da ni ba."

Kara karanta wannan

Wani ƙasurgumin ɗan ta'adda ya ajiye makamai, ya miƙa wuya ga rundunar sojoji a Arewa

- Nyesom Wike.

Wike ya yi shagube ga gwamnonin PDP

Tsohon gwamnan jihar Ribas ya taɓo gwamnonin PDP waɗanda ya yiwa barazanar kunno masu wuta idan suka tsoma baki a rikicin Ribas.

The Nation ta ruwaito Wike na cewa:

"Na faɗa masu idan suka sa hannu a sha'anin Ribas wuta za ta ƙona su, ga shi har sun fara kokawa, maimakon su maida hankali kan yadda za su ci zaɓe a jihohinsu, sun koma yin taruka a Taraba da Enugu, wa ya faɗi yanzu?"

Ya gargadi ‘yan siyasa da ke wajen jihar da su guji shiga harkokin siyasar Jihar Ribas, inda ya ce “Jihar Ribas ta musamman ce a gare ni.

Wike ya gana da ƴan BoT a Abuja

A wani rahoton kuma ministan Abuja, Nyesom Wike ya gana da ƴan majalisar amintattu na PDP (BoT) a daren ranar Talata, 17 ga watan Satumba 2024.

Legit Hausa ta fahimci cewa wannan taro wani wani ɓangare ne a yunƙurin BoT na kawo ƙarshen rigimar siyasar da ta dabaibaye jihar Ribas.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262