NTA: Shugaba Tinubu Ya Yi Sababbin Nade Naɗe 7 a Gwamnati, Sunaye Sun Bayyana

NTA: Shugaba Tinubu Ya Yi Sababbin Nade Naɗe 7 a Gwamnati, Sunaye Sun Bayyana

  • Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin manyan daraktoci bakwai a gidan taabijin na Najeriya (NTA)
  • Mai bai wa shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, ya sanar da haka ranar Jumu'a, 27 ga watan Satumba
  • Ya bayyana sunayen waɗanda aka naɗa da suka kunshi mutum ɗaya da aka sabunta naɗinsa da mutum shida da aka naɗa a karon farko

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya naɗa sababbin daraktoci bakwai a gidan talabijin na Najeriya watau NTA.

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar yau Jumu'a.

Kara karanta wannan

"An yiwa ƙasa addu'a": Tinubu ya haɗu da tsofaffin shugabanni 2 da sarki a masallacin Jumu'a

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.
Bola Tinubu ya naɗa manyan daraktoci a NTA Hoto: @aonanuga
Asali: Facebook

Channels tv ta ce a sanarwar mai taken, "Shugaban ƙasa Tinubu ya naɗa manyan daraktoci bakwai a NTA," Onanuga ya jero sunayen nutanen da Allah ya ci da su.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jerin sunayen waɗanda Tinubu ya naɗa

Sanarwar ta bayyana cewa Bola Tinubu ya amince da sake naɗin Ayo Adewuyi a matsayin babban daraktan sashen labarai na NTA.

Punch ta tattaro sauran waɗanda aka naɗa sababbi sun haɗa da:

1. Ibrahim Aliyu (lauya masanin harkokin shari'a - Daraktan sashen ayyuka na musamman.

2. Muhammed Mustapha - Daraktan gudanarwa da horarwa.

3. Mis Apinke Effiong - Darakta a sashen harkokin Kudi.

Ta kasance kwararriya a harkar hada-hadar kudi tare da ajiya, haka kuma tana da gogewa a ɓangaren gudanarwa da dabarun bayar da rahoto.

4. Mis Tari Taylaur - Babbar darakta a sashen shirye-shirye.

5. Mista Sadique Omeiza - Babban daraktan sashen gyare-gyare.

Kara karanta wannan

Damagum: Malami ya hango gwamnan da zai fice daga PDP zuwa wata jam'iyya

6. Misis Oluwakemi Fashina - Daraktan sashen kasuwaci da tallace-tallace. Tana da kwarewa a ɓangaren kasuwanci da mu'amala.

Majalisa ta tabbatar da naɗin CJN

A wani labarin kuma mai shari'a Kudirat Kekere-Ekun ta zama sabuwar shugabar alƙalan Najeriya watau CJN bayan tantancewa a majalisar dattawa.

Majalisar ta amince da buƙatar shugaban ƙasa Bola Tinubu, ta tabbatar da naɗin a zamanta na ranar Laraba, 25 ga watan Satumba, 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262