Tinubu Ya Shiga Tsaka Mai Wuya kan Korar Ministoci, an Taso Shi a Gaba

Tinubu Ya Shiga Tsaka Mai Wuya kan Korar Ministoci, an Taso Shi a Gaba

  • Yan siyasa da dama sun fara kama kafa tun bayan fitar da rahoto cewa Bola Tinubu ya shirya sallamar wasu ministocinsa
  • Wasu daga cikinsu sun fara neman yadda za a yi yaransu su tsallake wannan sauye-sauye da za a yi a gwamnatin Tinubu
  • Hakan ya biyo bayan samun labarin cewa shugaban zai yi garambawul domin kawo wasu sababbin jini a mukaman Ministoci

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Yayin da Shugaba Bola Tinubu ya sanar da shirin garambawul a gwamnatinsa, yam siyasa sun fara zirga-zirga.

Tun bayan sanarwa kan garambawul din, wasu ke neman ganin shugaban kasar domin tabbatar da zaman yaransu a gwamnatin.

Kara karanta wannan

Tinubu na kokarin canza ministoci, an kitsawa shugaban kasa juyin mulki a Benin

An fara kama kafa bayan shirin Tinubu na sallamar wasu Ministoci
Yan siyasa da dama sun fara nemawa yaransu Ministoci gindin zama a gwamnatin Bola Tinubu. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

An taso Tinubu a gaba kan Ministoci

Wata majiya ta tabbatarwa Punch cewa manyan yan siyasa sun fara kama kafa domin ganin wadanda suka kawo ko yaransu sun tsallake.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyar ta ce mafi yawansu sun kama kafa ne da na hannun daman Tinubu ciki har da shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila.

Har ila yau, wasu Ministoci da kansu suke neman gindin zama a wurin wasu daga cikin na hannun daman Tinubu.

Yadda yan siyasa ke damun Bola Tinubu

"Tabbas haka ne, wasu daga cikin Ministocin sun kira iyayen gidansu a siyasa domin su yi musu wani abu."
"Wannan ba sabon abu ba ne a gwamnati, amma Tinubu zai yi abin da ya dace ne domin tabbatar da inganta kasa."

- Cewar majiyar

Har ila yau, wata majiya ta ce Gbajabiamila ya fara nuna damuwa yadda ake damun Tinubu kan mukaman Ministoci domin sanin makomarsu.

Kara karanta wannan

Ta tabbata: Tinubu zai yiwa majalisar ministoci garambawul, za a runtuma kora

Majiyar ta ce saboda matsin lamba aka shawarci Tinubu ya wuce Burtaniya daga China domin ya samu sarari na yin tunani.

Tinubu ya yi magana kan korar Ministoci

Kun ji cewa fadar shugaban kasa ta tabbatar da cewa nan ba da jomawa ba za a yi wa majalisar ministocin tarayya garambawul.

Kakakin shugaban kasa, Bayo Onanuga, shi ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai a ranar Laraba 25 ga Satumbar 2024.

Onanuga ya ce watakila a yi garambawul din kafin 1 ga watan Oktoba ko bayan hakan yayin da Tinubu ya yi kira ga ministocin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.