‘Babu Maganar Zabe a 2027,’: Jigon PDP Ya Zargi APC da Shirya Maƙarƙashiya

‘Babu Maganar Zabe a 2027,’: Jigon PDP Ya Zargi APC da Shirya Maƙarƙashiya

  • Tsohon shugaban jam'iyyar PDP, Uche Secondus ya zargi jami'yyar APC da yaki da demokradiyya a zaben Edo na ranar Asabar
  • Secondus ya ce akwai alamun APC na son lalata dimokuraɗiyyar Najeriya wanda ba lallai a samu karfin gwiwar zaben 2027 ba
  • Tsohon shugaban ya kuma yi martani ga Abdullahi Ganduje kan cewa za su yi amfani da tsarin da suka yi a Edo a zabe mai zuwa a Ondo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Tsohon shugaban jam'iyyar PDP na kasa, Uche Secondus ya yi magana bayan zaben gwamna da ya gabata a jihar Edo.

Uche Secondus ya koka kan cewa sam ba a yi adalci a zaben ba, wanda ya ce hakan barazana ce ga dimokuraɗiyya.

Kara karanta wannan

Sanatan APC ya dura kan gwamna, ya ce ya mutu murus a siyasar Najeriya

Uche Secondus
Tsohon shugaban PDP ya ce APC ta lalata dimokuradiyya. Hoto: @PrinceUcheSecondus
Asali: Twitter

Vanguard ta wallafa cewa Uche Secondus ya kuma yi martani ga shugaban APC, Abdullahi Umar Ganduje.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jigon PDP ya nuna fargaba kan zaben 2027

Tsohon shugaban PDP na kasa, Uche Secondus ya ce ba lallai yan jam'iyyar adawa su samu kwanciyar hankalin yin zaɓe a shekarar 2027 ba.

Uche Secondus ya ce jam'iyyar APC ta dauko hanyar lalata dimokuraɗiyya ta yadda ba wani haske da suke gani da za a su iya samu a gaba.

Secondus ya ce ba a yi zabe a Edo ba

Uche Secondus ya ce abin da ya faru a Edo a ranar Asabar ba za a kira shi da zabe ba sai dai kwace mulki kawai.

Shugaban ya ce abubuwan da suke faruwa suna nuna cewa ana cigaba da samun maguɗi ne a zabe maimakon samun gyara.

Kara karanta wannan

Baki har kunne: Shugaban APC, Abdullahi Ganduje ya samu manyan nasarori a cikin mako 1

Tsohon shugaban PDP ya yi martani ga Ganduje

Uche Secondus ya ce maganar da Ganduje ya fada kan cewa za su yi amfani da tsarin zaben Edo a Ondo da Amambra bai dace ba.

Ya kara da cewa hakan na cikin alamun da suke nuna APC ta shirya maguɗi kuma haka za ta yi a shekarar 2027.

Yiaga ta ce an yi magudi a zaben Edo

A wani rahoton, kun ji cewa kungiyoyin sa-kai masu lura da yadda zaben gwamnan jihar Edo ya gudana a ranar Asabar sun fara fitar da rahoton bayan zabe.

Yiaga Africa ta fitar da rahoto kan yadda zaben ya gudana da kuma kura-kurai da ta ce an tafka a ɓangaren hukumar INEC ta kasa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng