Zaben Edo: Dan Takarar PDP Ya Fadi Wanda Zai Yi Nasara da Gagarumin Rinjaye

Zaben Edo: Dan Takarar PDP Ya Fadi Wanda Zai Yi Nasara da Gagarumin Rinjaye

  • Ɗan takarar gwamna na jam'iyyar PDP a jihar Edo ya kaɗa ƙuri'arsa a zaɓen na ranar Asabar, 21 ga watan Satumban 2024
  • Asue Ighodalo ya nuna ƙwarin gwiwar cewa shi ne zai samu nasara a zaɓen idan har ba a tafka maguɗin zaɓe ba
  • Ɗan takarar na PDP ya bayyana cewa bayanan da yake samu sun nuna cewa nasara ta shi ce a zaɓen gwamnan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Edo - Ɗan takarar jam'iyyar PDP a zaɓen gwamnan jihar Edo, Asue Ighodalo ya ce shi ne zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaɓen.

Asue Ighodalo ya bayyana hakan ne bayan ya kaɗa ƙuri'arsa a rumfar zaɓensa da ke makarantar firamare ta Indinrio a Okaigben Ewohomi cikin ƙaramar hukumar Esan ta Kudu maso Gabas ta jihar.

Kara karanta wannan

Zaben Edo: Oshiomole ya yi martani kan zargin APC na siyan kuri'u

Asue Ighodalo ya yi magana kan zaben Edo
Asue Ighodalo ya ce shi ne zai yi nasara a zaben gwamnan Edo Hoto: Asue Ighodalo
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust rahoto cewa Asue Ighodalo ya kaɗa ƙuri'ar ne tare da matarsa, Ifeyinwa Ighodalo da ƙaninsa, Fasto Ituah Ighodalo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Asue Ighodalo ya hango nasara a zaɓen Edo

Da yake magana da ƴan jarida, ɗan takarar gwamnan na PDP ya bayyana cewa yana da ƙwarin gwiwar yin nasara idan ba a yi maguɗi a zaɓen ba, rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

Asue Ighodalo ya kuma yabawa jami'an sojoji kan yadda suka samar da tsaro a lokacin zaɓen.

"Ina jin jita-jita cewa suna son murɗe zaɓen, amma bisa ga bayanan da nake samu, jam'iyyar PDP ce za ta lashe zaɓen.
"Zan kira wanda ya yi nasara a zaɓen idan an yi zaɓe na gaskiya da adalci, amma nine wanda za a kira."

- Asue Ighodalo

Oshiomole ya magantu kan zaɓen Edo

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon gwamnan jihar Edo, Sanata Adams Oshiomole, ya yi magana kan zargin APC ta shirya siyan ƙuri'u a zaɓen gwamnan jihar.

Adams Oshiomole ya musanta zargin cewa jam'iyyar ta tanadi tulin kuɗi domin amfani da su wajen siyan ƙuri'u a hannun mutane a lokacin zaɓen.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng