Tsofaffin Ƴan Majalisa da Wasu Kusoshi Sun Koma a APC, PDP Ta Yi Martani

Tsofaffin Ƴan Majalisa da Wasu Kusoshi Sun Koma a APC, PDP Ta Yi Martani

  • Wasu manyan kusoshin jam'iyyar PDP sun sauya sheka zuwa APC ranar Laraba, 18 ga watan Satumba, 2024 a jihar Ondo
  • Wannan sauya sheƙa dai ya ja hankalin jam'iyyar PDP, inda ta fito tana cewa dama can waɗanda suka koma APC sun zame mata ƙaya
  • Kwamitin kamfen PDP ya bayyana cewa masu sauya shekar ba za su tsinanawa APC komai ba face rashin nasara a zaɓe mai zuwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Ondo - Jam'iyyar PDP reshen jihar Ondo ta ce sauya shekar da wasu jiga-jiganta suka yi zuwa APC bai rage ta da komai ba.

A ranar Laraba ne wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP suka sanar da sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a jihar Ondo.

Kara karanta wannan

Kano: PDP na tsaka da kokarin warware rikicinta, 'yan jam'iyyar sun koma APC

Gwamna Lucky Aiyedatiwa.
PDP ta ce jiga-jiganta da suka sauya sheƙa ba za su taimaki Gwamna Aiyedatiwa da komai ba Hoto: Hon. Lucky Aiyedatiwa
Asali: Facebook

Ondo: Jiga-jigan PDP sun koma APC

Punch ta ce wasu daga cikin wadanda suka sauya shekar sun hada da tsohon dan majalisar tarayya Mista Akinlaja Joseph, Lad Alaba Ojomo da Victor Akinjo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sauran kusoshin PDP da suka bi sahu zuwa APC a Ondo sun haɗa da Gboluga Ikengboju da kuma tsohuwar kakakin majalisar dokokin jihar, Jumoke Akindele.

Duk da wannan koma baya, jam'iyyar PDP ta bayyana cewa babu tantama ɗan takararta ne zai lashe zaben gwamnan da za a yi ranar 16 ga watan Nuwamba a Ondo.

PDP ta mayar da martani kan sauya shekar

Mai magana yawun kwamitin kamfen ɗan takarar gwamna a PDP, Mr Ayo Fadaka, shi ya mayar da martani kan sauya sheƙar jiga-jigan a wata sanarwa.

A cewar sanarwar, waɗanda suka sauya shekar sun riga sun haɗe da APC tun kafin su sanar da barin PDP, don haka ba wani abin damuwa ba ne, in ji The Nation.

Kara karanta wannan

Edo 2024: Hankalin PDP ya tashi yayin da jam’iyyun siyasa 9 suka goyi bayan APC

"Mun lura cewa waɗannan mutane ƴan tsalle-tsalle ne daga wannan jam'iyya zuwa wata a duk lokacin da aka ce zaɓe ya matso, ba su iya zama wuri ɗaya.
"Ba za su tsinanawa Gwamna Lucky Aiyedatiwa da jam’iyyarsa komai ba, maimakon haka za su ƙara masa rashin sa'a, don haka muna taya gwamna da APC murna."

- Ayo Fadaka.

Gwamna Aiyedatiwa ya yi sabbin naɗe-naɗe

A wani rahoton kuma gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa ya sake zaɓo wasu mutane ya ba su muƙamai a gwamnatinsa.

Gwamnan ya naɗa sababbin hadimai mutum 344 waɗanda za su riƙa taimaka masa wajen gudanar da mulkin jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262