Kano: APC Ta Bugi Kirji kan Zaben Kananan Hukumomi, Ta Fadi Shirin da Ta Yi

Kano: APC Ta Bugi Kirji kan Zaben Kananan Hukumomi, Ta Fadi Shirin da Ta Yi

  • Shugaban jam'iyyar APC a Kano, Abdullahi Abbas ya bayyana shirin jam'iyyar game da zaben kananan hukumomi da za a yi
  • Abbas ya ce APC ta shirya shiga zaben kananan hukumomin Kano 44 da za a yi a ranar 24 watan Oktobar 2024 domin a dama da ita
  • Ya ce APC ta fara shiri wurin wayar da kan mambobinta domin shiga zaben, za a fara da yin zabukan fidda gwani na cikin jam'iyya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Jam'iyyar APC a jihar Kano ta yi magana kan zaben kananan hukumomi da za a yi.

Jam'iyyar ta ce a shirye ta ke a zaben da za a yi a jihar inda ta ce tana sa ran samun nasara a zaben ranar 24 ga watan Oktobar 2024.

Kara karanta wannan

Zaben Edo: APC ta fasa sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya

APC ta shirya game da zaben kananan hukumomi a Kano
Jam'iyyar APC ta sha alwashi kan zaben kananan hukumomi a jihar Kano. Hoto: @Kyusufabba, @officialAPCNg.
Asali: Twitter

Kano: APC ta shiryawa zaben kananan hukumomi

Shugaban jam'iyyar APC a Kano, Abdullahi Abbas ya tabbatar da haka ga manema labarai a yau Alhamis 12 ga watan Satumbar 2024, cewar rahoton Punch.

Abbas ya ce yanzu haka sun shirya za su gudanar da zabukan fidda gwani a jihar domin fitar da yan takara.

Ya ce APC ta fara hada kan yan jam'iyyar tare da wayar da kansu domin fita zaben da za a gudanar, Daily Post ta ruwaito.

Jam'iyyar APC ta roki hukumar zaben jihar Kano

"Mu na yin duk mai yiyuwa domin ganin dubban magoya bayanmu sun shiga an dama da su a zaben kananan hukumomi."
"Mu na kira ga hukumar zaben jihar Kano da ta ba kowa dama domin gudanar da zaben cikin lumana da adalci."

Kara karanta wannan

NNPP ta fito da mace a matsayin 'yar takarar shugaban karamar hukumar Kano

- Abdullahi Abbas

A ranar 26 Oktoba ne hukumar zaben mai zaman kanta ta Kano (KANSIEC) za ta gudanar da zabukan kananan hukumomi a jihar.

Mace za ta zama 'yar takara a Kano

Kun ji cewa jam'iyya mai mulki a Kano ta fitar da yan takara akalla 484 a zaben kananan hukumomi da za a gudanar nan gaba kadan.

Daga cikin masu neman mukamai daban-daban, NNPP ta tsayar da mace guda daya, Sa'adatu Salisu a takarar shugabar karamar hukuma.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.