Dan Majalisar Tarayya a Arewa Ya Shiga Matsala, Mazabarsa na Shirin Masa Kiranye

Dan Majalisar Tarayya a Arewa Ya Shiga Matsala, Mazabarsa na Shirin Masa Kiranye

  • Dan Majalisar Tarayya a jihar Yobe, Hon. Lawan Shettima Ali yana fuskantar matsala bayan shirin yi masa kiranye
  • Yan mazabar Ngazargamu da ke jihar Yobe sun nuna damuwa kan yadda dan Majalisar ya yi fatali da su a yankin
  • Wasu jagororin da ke mazabar Geidam da Yunusari da Bursari sun fadi shirinsu na yin kiranye ga dan Majalisar nasu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Yobe - Wasu mazauna mazabar Ngazargamu daga jihar Yobe sun fusata da dan Majalisarsu da ke Tarayya.

Hon. Lawan Shettima Ali yana fuskantar barzanar bayan yan mazabar sun tabbatar da cewa bai tabuka musu komai ba.

Ana shirin yi wa dan Majalisar Tarayya kiranye
Dan Majalisar Tarayya a jihar Yobe, Hon. Lawan Shettima Ali na fuskantar barazanar kiranye. Hoto: Hassan Ibrahim Gumsa.
Asali: Facebook

'Dan Majalisa na fuskantar barazana a Yobe

Kara karanta wannan

Bayan ambaliya a Borno da Bauchi, an shiga fargaba a garuruwan Yobe

Jagororin mazabar da suka hada da Geidam da Yunusari da Bursari sun tabbatar da hakan ga jaridar Aminiya.

Suna zargin dan Majalisar da yin fatali da su tare da wucewa birnin Abuja inda ya mance da su gaba daya.

Wani daga cikin jagororin, Babagana Aisami Geidam ya sanar da yan yankin cewa suna shirin yi wa dan majalisarsu kiranye saboda rashin jagorranci nagari.

Aisami ya kuma zargi dan Majalisar da rashin gabatar da wani kudiri kan matsalolin yankin da suke fama da shi.

Musabbabin shirin yin kiranye ga dan majalisa

"Tafiya ta yi nisa wajen wannan shiri, muna aiki tuƙuru ba dare ba rana domin tabbatar da wannan aikin don samarwa al’umma mafita.”
"Yankin na Ngazargamu ya sha fama da matsalolin tsaro, wanda ya haifar da koma baya ta fuskar ilimi da tattalin arziƙi da noma da sauran fannonin rayuwa."

Kara karanta wannan

Ambaliya: Mutane sama da 200,000 sun rasa gidaje, yara sun bace a Maiduguri

.- Babagana Aisami

Aisami ya ce amma duk da wadannan tarin matsalolin, dan Majalisar ya kasa kawo sauyi a rayuwar al'umma.

Sarkin Potiskum ya ziyarci Sanusi II

Kun ji cewa Sarkin Potiskum da ke jihar Yobe, Umar Bauya ya kai ziyarar goyon baya ga Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II.

Basaraken ya ce ya zo fadar Sanusi II ne domin yin mubaya'a da nuna goyon baya a gare shi da mutanensa baki daya.

Sarkin ya roki Sanusi II da ya ba da gudunmawarsa wurin karasa gina masallacin Juma'a da suka faro shekarun baya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.