Gwamna Abba Ya Sake Rusa Aikin Ganduje, Ya Maido Makarantun Kwanan Mata 15

Gwamna Abba Ya Sake Rusa Aikin Ganduje, Ya Maido Makarantun Kwanan Mata 15

  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dawo da makarantun kwana 15 na mata waɗanda AbdullahuGanduje ya soke a zamanin mulkinsa a Kano
  • Abba ya bayyana cewa tuni shirye-shirye suka yi nisa na sake mayar da makarantun na kwana kamar yadda aka sansu a baya
  • Gwamnan ya faɗi haka ne a lokacin ziyara ba zata domin duha aiki a makarantar sakandiren Mata da ke ƙaramar hukumar Albasu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Gwamna Abba Kabir Yusuf na Kano ya soke matakin da tsohon gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ɗauka na canza wasu makarantun kwana 15 zuwa na jeka ka dawo.

Gwamma Abba ya ce gwamnatinsa ta maido da makarantun sakandiren guda 15 na mata zuwa matsayinsu na makarantun kwana.

Kara karanta wannan

"Ka da ku ɗagawa kowa ƙafa," Gwamma Abba ya kafa kwamiti kan abin da ya faru a Kano

Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Gwamna Abba ya maido da makarantun kwana na mata waɗanda Ganduje ya soke a Kano Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Twitter

Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, shi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Abba ya maido da wasu makarantun kwana

Abba Kabir ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar ba zata makarantar sakandiren mata ta gwamnati da ke karamar hukumar Albasu a jihar Kano.

Gwamnan ya nuna matuƙar ɓacin ransa kan cire makarantun daga tsarin karatun kwana, inda ya ce hakan ya daƙile wasu ɗalibai mata masu hazaƙa.

Ya kuma umarci ma'aikatar ilimi ta jihar Kano ta gaggauta tura malaman lissafi, turanci da na kimiyya zuwa makarantar sakandiren mata da ke Albasu.

Gwamma Abba ya ce aiki ya yi nisa na sake maido da makarantun su koma na kwana kamar yadda aka sansu a baya.

Kara karanta wannan

Gwamna Abba Gida Gida ya fusata da aiki, ya kwace kwangilar titi a Kano

A cewarsa, gwamnatin Kano ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen sabunta ajujuwa da gina sababbi domin samar da yanayi mai kyau na koyo da koyarwa a makarantu.

Gwamnan Kano ya yaba da aikin titin Albasu

Abba Kabir Yusuf ya kuma duba aikin gina titin zuwa Albasu mai tsawon kilomita biyar, wanda ya zu haka ake dab da kammalawa.

Gwamnan ya yaba da yadda ya ga aikin sannan ya roki ɗan kwangilar ya ƙara azama domin ƙarasa aikin cikin ƙanƙanin lokaci.

Gwamnatin Kano ta kama shugaban makaranta

Kuna da labarin gwamnatin Kano ta cafke wani shugaban makarantar firamare bisa zargin cefanar da wasu cikin kayan da aka zuba a makarantar.

Hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa (PCACC) ce ta kama malamin makarantar firamaren Gaidar Makada.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262