"Arewa Ta Yi Hakuri," Sanatan Kaduna Ya Faɗi Wanda Ya Kamata Mutane Su Zaɓa a 2027

"Arewa Ta Yi Hakuri," Sanatan Kaduna Ya Faɗi Wanda Ya Kamata Mutane Su Zaɓa a 2027

  • Shehu Sani ya bayyana cewa kamata ya yi Arewa ta hakura ta bar ƴan Kudu su ci gaba da mulkin Najeriya a babban zaɓen 2027
  • Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya ya ce daga nan kuma Arewa za ta samu cikakkiyar damar samar da shugaban ƙasa a 2031
  • Ya ƙara da cewa Bola Tinubu ya cancanci ya kara samun goyon bayan ƴan Arewa saboda abin da ya yi masu lokacin zaben 2015

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna - Tsohon sanatan Kaduna da tsakiya, Shehu Sani ya tsoma baki kan muhawarar da ake ta yi kan tazarcen shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu a 2027.

A cewar Shehu Sani, kundin tsarin mulkin kasa ya bai wa kowane dan Najeriya damar tsayawa takara kuma ko daga wane yanki ya fito.

Kara karanta wannan

Malami ya bayyana hanya 1 da za a iya kayar da Shugaba Tinubu a zaɓen 2027

Shehu Sani da Bola Tinubu.
Sanata Shehu Sani ya faɗi abin da.ya kamata ƴan Arewa su yi a zaɓen 2027 Hoto: Shehu Sani, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Sanatan ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da wakilin jaridar Punch a Kaduna ranar Alhamis, 29 ga watan Agusta, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shehu Sani ya faɗi ra'ayinsa kan zaɓen 2027

Ya ƙara da cewa kamata ya yi a bar ƴan Kudancin Najeriya su sake neman takara a 2027, wanda hakan zai ba Arewa damar samar da shugaban ƙasa a 2031.

Sanata Shehu Sani ya ce:

"A nawa ra'ayin, kamata ya yi a bar ƴan Kudu su ci gaba da mulki a 2027, ko shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya yi tazarce, ko Peter Obi ko tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan."
"Daga nan kuma Arewa zata samu cikakkiyar damar samar da shugaban ƙasa na gaba a 2031," in ji Shehu Sani.

'Dalilin Arewa na sake zaɓen Tinubu'

Sai dai tsohon sanatan ya ƙara da cewa zai fi kyau Arewa ta marawa Shugaba Tinubu baya fiye da kowane ɗan Kudu saboda shi ne mutum ɗaya tilo da ya tsaya masu.

Kara karanta wannan

Tsohon kakakin jam'iyyar APC ya tarewa Atiku Abubakar faɗa kan takara a 2027

Tsohon sanatan kuma jigo a PDP ya ce tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari ya nemi takara sau da dama amma bai yi nasara ba sai da ya haɗe da Tinubu.

Sanata Shehu Sani ya shawarci gwamnatin Bola Tinubu ta maida hankali wajen magance matsalar tsaro, fatara da jahilci a Arewa saboda a sake zaɓensa a 2027.

Ya kuma kara da cewa kwadayin da wasu jiga-jigan siyasar Arewa suke yi na kwace mulki bai dace da ra'ayin ƴan Arewa ba illa dai wasu dalilai ne na kashin kansu, rahoton Vanguard.

Da wahala ƴan Arewa su yi Tinubu

Wasu ƴan Arewa sun shaidawa Legit Hausa cewa ba za su sake zaɓen Bola Tinubu ba domin a yanzu ma sun fara nadamar goyon bayan da suka ba shi.

Abdulhafiz Abdullahi ya ce duk idan ya tuna cewa Tinubu ya zaɓa ya kan ji nadama da takaici saboda halin ƙuncin da ake ciki.

Kara karanta wannan

Sojoji sun kashe ƴan bindiga sama da 1,000, sun ceto ɗaruruwan mutane a Najeriya

"Duk yadda muka tsani Buhari daga ƙarshe ashe gara shi, wallahi mutane suna cikin wahala, ni dai a karan kaina ba zan ƙara zaɓen Tinub ba," in ji shi.

Haka nan wani ɗan APC a Katsina, Usman Ahmad ya ce ya yi wuri a fara magana kan wanda ya kamata a zaɓa a 2027.

APC na shirin ƙwace jihohin Najeriya

A wani rahoton kuma shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa jam'iyyar na shirin ganin jihohin Najeriya 36 sun dawo hannunta.

Ganduje ya nuna ƙwarin gwiwar cewa APC za ta lashe zaɓukan gwamna a jihar Ondo da Edo waɗanda za a yi a wannan shekarar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262