2027: Tinubu Ya Nemo Hanyar Shawo kan Yan Arewa, an Fadi Dabarun da Ya Shirya

2027: Tinubu Ya Nemo Hanyar Shawo kan Yan Arewa, an Fadi Dabarun da Ya Shirya

  • Yayin da aka fara tunanin zaben 2027 tun yanzu, wasu shugabannin yankin Arewacin kasar sun fara korafi da gwamnatin APC
  • Dalilin haka ne ma ya sanya Shugaba Bola Tinubu daukar wasu matakai domin shawo kan korafe-korafen daga Arewa
  • Hakan bai rasa nasaba da matsalolin da yankin ke fama da su da ake ganin zai iya jawowa Bola Tinubu matsala a zaben 2027

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Da alamu Shugaba Bola Tinubu ya fara shirye-shiryen daukar matakai game da zaben 2027.

Ana hasashen Tinubu ya fara shirin ne da wuri domin shawo kan shugabannin Arewa da suke kushe salon mulkinsa.

Kara karanta wannan

An yi korafin yadda Tinubu ya 'hana' Kashim Shettima rantsar da Shugabar Alkalai

Tinubu ya shirya lallbar yan Arewa a zaben 2027 da ke tafe
Shugaba Bola Tinubu ya fara shiri kan zaben 2027 da lallabar yan Arewa. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

2027: Tinubu ya fara shiri kan yan Arewa

A wani rahoto da Punch ta fitar na musamman a yau Lahadi 25 ga watan Agustan 2024, an bayyana irin shirin da shugaban ke yi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wata majiya ta bayyana irin tsare-tsaren da aka kaddamar tare da kirkirar wasu sababbi saboda shawo kan matsalolin.

Majiyar ta tabbatar da cewa Tinubu bai tsoron masu cece-kuce amma an dauki matakan ne domin shawo kan shugabannin yankin da ke kalubalantar zabensa a 2027.

2027: Matakai 2 da Tinubu ya dauka

"Farkon abin da za a fara yi shi ne kara mukamai a yankin Arewacin Najeriya, idan an yi haka akwai yiwuwar a rufe bakin masu korafi kan haka."
"Na biyu, shi ne dakile matsalolin rashin ilimi da talauci wanda shi ne musabbabin kirkirar hukumar Arewa maso Gabas (NEDC)."

- Cewar majiyar

Kara karanta wannan

Mutumin Jonathan ya tono makircin da ake shiryawa Tinubu a Arewa bayan sayen jirgin sama

Majiyar ta tabbatar da cewa an dauki wasu matakai guda biyu domin kwantar da hankula a Arewa saboda zaben 2027 da ake tunkara.

Arewa: An shawarci Tinubu kan zaben 2027

Kun ji cewa Jigon jam'iyyar PDP a Najeriya, Abdul-aziz Na'ibi Abubakar ya yi tsokaci kan zaben 2027 da 'yan Arewa.

Abdul-aziz ya ce Bola Tinubu ba zai taba samun kuri'un 'yan Arewa ba musamman bayan sanya hannu a yarjejeniyar Samoa.

Na'ibi ya ce zai yi wahala yankin Kudu maso Yammacin Najeriya su iya kawo Tinubu a zaben domin ba shi dama ta biyu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.