Rikici Ya Dawo Ɗanye, An Fara Shirin Waje da Gwamnan Jam'iyyar PDP a Najeriya

Rikici Ya Dawo Ɗanye, An Fara Shirin Waje da Gwamnan Jam'iyyar PDP a Najeriya

  • Ga dukkan alamu babu ranar sasanta rikicin siyasar jihar Ribas yayin da ƴan NWC PDP suka fara haɗa kai da ministan Abuja, Nyesom Wike
  • Rahotanni sun nuna rikicin ya raba kawunan shugabannin PDP na ƙasa, tsagi ɗaya na tare da Wike yayin da sauran ke goyon bayan Fubara
  • Kwamitin gudanarwa na PDP ta ƙasa (NWC) ya gudanar da taro kwanan nan domin tattauna halin da jam'iyyar ke ciki a jihar Ribas

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rivers - Wasu daga cikin mambobin kwamitin gudanarwa (NWC) na PDP ta ƙasa sun fara haɗa kai da ministan Abuja, Nyesom Wike domin tsige gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki biyu bayan kwamitin amintattun PDP sun kaiwa Gwamna Fubara ziyara, inda suka ce ba za su bari Ribas su suɓuce masu ba.

Kara karanta wannan

Wike ya yi maganar yiwuwar sasantawa kan rikicinsa da Gwamna Fubara

Nyesom Wike da Siminalayi Fubara.
Wasu ƴan NWC na PDP sun juyawa Gwamna Fubara baya a rikicinsa da Nyesom Wike Hoto: Nyesom Ezenwo Wike, Siminalayi Fubara
Asali: Facebook

A rahoton da Punch ta tattara ranar Alhamis, 22 ga watan Agusta, 2024, rikicin siyasar da ke faruwa a Ribas ya raba kawunan shugabannin PDP na ƙasa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rivers: An sabunta shirin tsige Fubara

Wani babban ƙusa a NWC ya bayyana cewa akalla shugabanni 12 na PDP na bin umarnin Nyesom Wike wajen takun saƙa da Gwamna Fubara.

Wadanda ake zargin suna da hannu a shirin sauke Gwamna Fubara sun haɗa da sakataren PDP na ƙasa, Samuel Anyanwu da sakataren tsare-tsare, Umar Bature.

Mataimakin sakataren PDP na ƙasa, Setonji Koshoedo da wasu mambobin NWC takwas na cikin waɗanda suka koma tsagin Wike a rigimar siyasar Ribas.

Mambobi NWC 3 na tare da Fubara

Duk da wannan shiri da suke yi, mutum uku daga cikin mambobin NWC da suka haɗa da mai ba da shawara kan harkokin shari'a, Debo Ologunagba, sun ce suna goyon bayan Fubara.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya faɗi gaskiya kan jita jitar yana shirin sauya sheƙa

Kazalika wata majiya daga NWC PDP ta ƙara da cewa a halin yanzu jam'iyyar reshen jihar Ribas za ta ci gaba da gudanar da harkokinta ƙarƙashin Wike, Leadership ta kawo.

Gwamna Fubara ya musanta barin PDP

Ku na da labarin Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas ya tabbatar da cewa yana nan daram a matsayin ɗan jam'iyyar PDP kuma ba shi da shirin sauya sheka.

Fubara ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi bakuncin tawagar kwamitin amintattun PDP karkashin jagorancin Adolphus Wabara.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262