Rahoto: Kotun Koli Ta Fara Zaman Karshe Kan Shari'ar Zaben Gwamnan Kogi da Bayelsa

Rahoto: Kotun Koli Ta Fara Zaman Karshe Kan Shari'ar Zaben Gwamnan Kogi da Bayelsa

Abuja – Kotun Koli ta fara zaman karshe kan rigingimun da suka kunno kai bayan kammala zaben wasu jihohi da ba a yi su tare da babban zaben 2023 ba.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kamar yadda rahotanni suka bayyana a ranar Litinin, 19 ga watan Agusta, 2024, zaman kotun ya shafi kararrakin zaben zaben jihohin Kogi da Bayelsa a watan Nuwamba 2023.

Kotun Koli ta fara zaman karshe kan shari'ar zaben gwamnan jihar Kogi, Bayelsa
Kotun Koli ta ci gaba da sauraron shari'ar ggwamnan Kogi da Bayelsa, yau za a kulle jawabai. Hoto: @OfficialOAU, @govdouyediri, @inecnigeria
Asali: Twitter

Rahoton Channels TV ya nuna cewa hukumar INEC ta bayyana Usman Ododo ne ya lashe zaben gwamnan Kogi, sai kuma Duoye Diri ya yi nasara a Bayelsa.

Legit Hausa ta ruwaito Gwamna Ododo ya yi nasara a karkashin jam'iyyar APC ne yayin da Gwamna Diri ya ci zabe a karkashin jam'iyyar PDP.

Kara karanta wannan

Jihar Kudu ta nemi daukin shugaban APC Ganduje domin ceto siyasar Tinubu a 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A Kogi, Muritala Ajaka na jam’iyyar SDP na kalubalantar sanarwar da INEC ta yi kan sakamakon zaben jihar.

Hakazalika, tsohon gwamnan Bayelsa, kuma tsohon ministan albarkatun man fetur, Timipre Sylva (APC), na neman Kotun Koli ta soke nasarar Gwamna Diri.

Za mu ci gaba da kawo maku karin bayani...

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.