NEC: Ana Rade Radin Kwace Kujerar Ganduje, APC Ta Tsaida Ranar Taron da Ake Jira

NEC: Ana Rade Radin Kwace Kujerar Ganduje, APC Ta Tsaida Ranar Taron da Ake Jira

  • Ana cikin jita-jitar sauyawa Abdullahi Ganduje mukami, jam'iyyar APC ta sanar da shirya babban taronta na Majalisar zartarwa
  • Jam'iyyar APC ta sanya 12 ga watan Satumbar 2024 a matsayin ranar gudanar da taron NEC a birnin Tarayya, Abuja
  • Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mataimakin sakataren jam'iyyar, Fetus Fuanter ya fitar a yau Alhamis

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Jam'iyyar APC mai mulkita sanya ranar gudanar da babbar taronta na Majalisar zartarwa (NEC).

Jam'iyyar ta sanya ranar 12 ga watan Satumba 2024 domin gudanar da ganawar a birnin Tarayya, Abuja.

APC ta sanya ranar gudanar da babban taron NEC a Abuja
Jam'iyyar APC a Najeriya ta sanya ranar gudanar da taron NEC. Hoto: All Progressives Congress.
Asali: Facebook

NEC: An sanya ranar taron jam'iyyar APC

Kara karanta wannan

Yan sanda da matasa sun mamaye sakatariyar jam'iyyar APC, bayanai sun fito

Daily Trust ta ce ganawar NEC ita ce ta biyu mafi girma daga cikin tarurruka da ake daukar wasu muhimman matakai.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mataimakin sakataren jam'iyyar, Barista Fetus Fuanter shi ya tabbatar da haka a yau Alhamis 15 ga watan Agustan 2024.

Fuanter ya ce masu ruwa da tsakin jam'iyyar za su gana a ranar 11 ga watan Satumba kafin gudanar da taron a washe-gari.

Ya ce a taron nasu sun goyi bayan kasancewar Cif Tony Okocha shugaban riko na jam'iyyar a jihar Rivers inda ya cancanci hukuncin kotu da ta kare shi.

Ganduje na iya rasa kujerar shugaban APC

Wannan na zuwa ne yayin da ake jita-jitar Shugaba Bola Tinubu zai sauyawa Abdullahi Ganduje muƙami.

Rahotanni sun tabbatar da cewa Tinubu zai mayar da Ganduje muƙamin jakada a daya daga cikin ƙasashen Nahiyar Afirka.

Kara karanta wannan

Kotu ta kori korafin yan takarar APC da NNPP, ta fadi wanda ya lashe zaben Sanata

Wata majiya ta ce hakan bai rasa nasaba da zarge-zargen cin hanci da rashawa da ake yi kan Ganduje a jihar Kano.

Zanga-zanga: Ganduje ya jefi Abba da zargi

Kun ji cewa Shugaban jam'iyyar APC a Najeriya, Abdullahi Ganduje ya yi magana kan zanga-zanga da aka yi a jihar Kano.

Ganduje ya ce ya samu bayanan sirri masu muhimmanci da ke tabbatar da Abba Kabir ne ya dauki nauyin zanga-zangar.

Hakan ya biyo bayan zargin da Gwamna Abba Kabir ya yi cewa wasu matasa da aka ɗauki hayarsu sun da e takardun shari'ar Ganduje.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.