Zaben 2027: Yaron El Rufai Ya Yi Martani Kan Batun Hadakar Mahaifinsa da Peter Obi

Zaben 2027: Yaron El Rufai Ya Yi Martani Kan Batun Hadakar Mahaifinsa da Peter Obi

  • Ɗan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, Bashir El-Rufai, ya musanta raɗe-raɗin yin haɗaka tsakanin mahaifinsa da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi
  • Ya bayyana jita-jitar a matsayin ƙarya ce tsagwaronta a martanin da ya wallafa a shafinsa na X bayan wani ya yi iƙirarin cewa ƴan siyasan biyu za su yi haɗaka
  • An yi ta raɗe-raɗin cewa akwai rashin jituwa tsakanin El-Rufai da Bola Tinubu bayan majalisar dattawa ta ƙi amincewa da naɗinsa domin zama minista

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Bashir El-Rufai, ɗaya daga cikin ƴaƴan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi magana kan yiwuwar yin haɗaka tsakanin mahaifinsa da Peter Obi.

Kara karanta wannan

Gwamnoni sun shiga sabuwar matsala bayan SERAP ta hada su da Tinubu

Bashir El-Rufai ya yi watsi da raɗe-raɗin da ke cewa mahaifinsa zai yi haɗaka da ɗan takarar na zaɓen shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour Party (LP), Peter Obi.

El-Rufai da Peter Obi
Ana rade-radin El-Rufai zai yi hadaka da Peter Obi Hoto: PATRICK MEINHARDT/AFP, PIUS UTOMI EKPEI/AFP
Asali: Getty Images

El-Rufai ya samu saɓani da Tinubu

El-Rufai ya taka rawar gani a kan nasarar da Shugaba Bola Tinubu ya samu a zaɓen 2023, sannan an zaɓe shi domin samun kujerar minista.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai, majalisar dattawa ta ƙi amincewa da naɗin da Shugaba Tinubu ya yi masa.

Tun a wancan lokaci ake ta raɗe-raɗin cewa alaƙar siyasa tsakanin tsohon gwamnan na Kaduna da Tinubu ta ruguje, kuma yana iya yin adawa da shugaban ƙasan idan ya nemi tazarce a zaɓen 2027.

Bashir El-Rufai ya yi martani kan haɗakar El-Rufai da Peter Obi

A na cikin wannan raɗe-raɗin, wani mai amfani da sunan Hon. Dan_Borno, @DanBornoReal, a shafin X, wanda ya bayyana kansa a matsayin ɗan gwagwarmayar siyasa ya ce akwai yiwuwar haɗaka tsakin El-Rufai da Peter Obi.

Kara karanta wannan

Obasanjo ya yi sabuwar fallasa kan majalisar dattawa da ta wakilai

"Akwai jita-jita na yiwuwar yin haɗaka tsakanin Peter Obi da Nasir Ahmed El-Rufai."

- Hon. Dan_Barno

Da yake mayar da martani a shafinsa na X Bashir El-Rufai ya musanta hakan.

"Ƙarya ce tsagwaronta daga kogin Ezu a Anambra."

- Bashir El-Rufai

Karanta wasu labaran kan El-Rufai

Kwankwaso ya gayyaci El-Rufai

A wani labarin kuma, kun ji cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi magana kan bude kofa da suka yi ga duk mai son shiga jam'iyyar NNPP.

Kwankwaso ya ce suna maraba da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai idan zai shigo jam'iyyar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng