"Gidan Yari Ya Dace da Su": Obasanjo Ya Koka Kan Halin Shugabanni

"Gidan Yari Ya Dace da Su": Obasanjo Ya Koka Kan Halin Shugabanni

  • Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya fadi yadda yan siyasa da shugabanni ya kamata su kasance yayin jagoranci
  • Obasanjo ya ce mafi yawansu ba su da tarbiyya ko halayya na kwarai saboda ba gyaran kasa ba ne a gabansu
  • Ya ce mafi yawansu sun fi dacewa a kulle su a gidajen gyaran hali saboda salon yadda suke gudanar da mulki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana takaici yadda shugabanni ke gudanar da mulki a yanzu.

Obasanjo ya ce ya kamata mafi yawansu suna garkame a gidan yari ne madadin rike da manyan ofisoshin gwamnati.

Kara karanta wannan

Tsohon shugaban ƙasa ya aike da saƙon gaggawa ga Tinubu kan masu zanga zanga

Obasanjo ya fadi inda ya kamata a jefa yan siyasar Najeriya
Cif Olusegun Obasanjo ya bukaci shugabanni su zama masu gaskiya a Najeriya. Hoto: Getty Images.
Asali: Getty Images

Obasanjo ya Allah wadai da halin shugabanni

Tsohon shugaban ya bayyana haka ne a birnin Abeokuta da ke jihar Ogun yayin ganawa da mambobin Majalisar Tarayya, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Obasanjo ya ce mafi yawan shugabanni a yanzu ba su da tarbiyya da kuma gaskiya da ya kamata su jagoranci Najeriya, Daily Trust ta tattaro.

Ya ce ya kamata a sake zama kan tsarin shugabanci da ake gudanarwa a yanzu musamman da ke karkashin jagorancin gurbatattun shugabanni.

Obasanjo ya fadi inda ya dace da shugabanni

"Ya kamata mu sake zama kan tsarin mulkin da ake bi, amma babu gaskiya da kuma amana ga wadanda ke mulkarmu, cikin girmamawa gaskiya ya kamata suna gidan yari ne ko a rataye su."
"Idan irin wadannan shugabannin ne ke mulkarmu ta yaya kake tsammanin a samu cigaba."

Kara karanta wannan

Obasanjo ya gargadi shugabanni, ya fadi abin da zai samu Najeriya nan gaba

"Abin da aka fi buƙata shi ne halayyarsu da kuma gaskiya da rikon amana."

- Cif Olusegun Obasanjo

Obasanjo ya tona asiri kan tallafi mai a Najeriya

Kun ji cewa tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya ce ana cigaba da biyan kudin tallafin mai a boye duk da cirewa da aka yi.

Obasanjo ya koka kan yadda ake cikin matsin halin kunci da kuma tsadar rayuwa wanda ya tilasta fara zanga-zanga a fadin kasar.

Tsohon shugaban kasar ya ce matasa da suke zanga-zanga neman hakkinsu suke duba da halin matsin da aka jefa su ciki na tsadar rayuwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.