Tsohon Shugaban Ƙasa Ya Aike da Sakon Gaggawa Ga Tinubu Kan Masu Zanga Zanga

Tsohon Shugaban Ƙasa Ya Aike da Sakon Gaggawa Ga Tinubu Kan Masu Zanga Zanga

  • Cif Olusegun Obasanjo ya gargaɗi gwamnatin tarayya ta biya bukatun matasa masu zanga zanga saboda suna kan gaskiya
  • Tsohon shugaban kasar ya ce Najeriya ta samu koma baya bayan ya bar mulki saboda waɗanda suka biyo bayansa ba su yi abin da ya dace ba
  • Obasanjo ya bayyana haka ne yayin da ya karɓi bakuncin ƴan majalisar wakiali shida a gidansa da ke Abeokuta a jihar Ogun

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ogun - Tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo ya ce matasan da suka fita zanga-zanga kan tsadar rayuwa suna kan gaskiya kuma ya kamata a saurari kokensu.

Obasanjo ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya karbi bakuncin ‘yan majalisar wakilai shida wadanda suka kai kudirin dokar wa’adi daya na shekara shida ga shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan

Obasanjo ya gargadi shugabanni, ya fadi abin da zai samu Najeriya nan gaba

Bola Tinubh da Olusegun Obasanjo.
Obasanjo ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Tinubu ya saurari buƙatun masu zanga zanga Hoto: @OfficialABAT@Oolusegun_obj
Asali: Twitter

Daily Trust ta ce ƴan majalisar sun buƙaci rika karɓa-karɓa tsakanin Arewa da Kudu, sannan kujerar gwamna ta rika kewaya wa tsakanin mazaɓun sanatoci uku a kowace jiha.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

‘Yan majalisar dai sun gana da Obasanjo ne ƙarƙashin jagorancin Hon. Ugochinyere Ikenga mai wakiltar mazabar Ideato ta Arewa da Ideato ta Kudu a jihar Imo.

A jawabinsa, Obasanjo ya ce gwamnatocin da suka shuɗe sun sauka daga kan tubalin da ya kafa a lokacin mulkinsa, yana mai cewa hakan ya jawo koma baya.

Zanga-zanga: Obasanjo ya ba Tinubu mafita

"Abubuwan da matasa masu zanga-zanga suka buƙata bai saɓa doka ba kuma ya kamata a saurare su da kunnen basira, taya ƙiri-ƙiri za a ƙwace masu abin da dama mallakinsu ne?
"Suna cikin takaici da ƙuncin rayuwa, suna jin yunwa, sun fusata, ba su da aikin yi, sun cancanci a zauna a saurare su," in ji Obasanjo a gidansa da ke Abeokuta, jihar Ogun.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Tsohon shugaban ƙasa ya gana da ƴan Majalisar Tarayya 6, bayanai sun fito

Tsohon shugaban ƙasar ya buƙaci gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta biyan buƙatun matasan da ke zanga-zanga a kasar nan domin su na kan gaskiya, in ji PM News.

Obasanjo ya ja kunnen shugabanni

A wani rahoton kuma tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya gargadi shugabanni a kasar nan kan matsalar da ke tunkaro wa

Dattijon kasar ya yi gargadin cewa Najeriya ba za ta cigaba ba matukar shugabanni da 'yan kasa ba za su rungumi hakuri ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262