Zanga Zanga: Tsohon Shugaban Ƙasa Ya Gana da Ƴan Majalisar Tarayya 6, Bayanai Sun fito

Zanga Zanga: Tsohon Shugaban Ƙasa Ya Gana da Ƴan Majalisar Tarayya 6, Bayanai Sun fito

  • Ƴan majalisar tarayya shida karƙashin jagorancin Hon. Ikenga Ugochinyere sun yi ganawar sirri da Olusegun Obasanjo a Abeokuta
  • Bayanai sun nuna tsohon shugaban ƙasar ya tattauna muhimman batutuwa da suka shafi Najeriya a wannan taro na ranar Jumu'a
  • Wannan dai na zuwa ne bayan abubuwa marasa daɗi da suka faru a sƙasar nan lokacin zanga zangar adawa da manufofin gwamnnati

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abeokuta, Ogun - Tsohon shugaban ƙasa, Cif Olusegun Obasango ya yi ganawar sirri da ƴan majalisar wakilai shida a Abeokuta, babban birnin jihar Ogun

Ƴan majalisar sun shiga wannan taro wanda ke gudana a gidan Obasanjo ƙarƙashin jagorancin Hon. Ikenga Ugochinyere, mai wakiltar mazaɓar Ideato ta Kudu da ta Arewa.

Kara karanta wannan

Tsohon shugaban ƙasa ya aike da saƙon gaggawa ga Tinubu kan masu zanga zanga

Tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo.
Yan majalisa 6 sun shiga ganawa da tsohon shugaban kasa a Ogun Hoto: Chief Olusegun Obasanjo
Asali: Getty Images

Me za a tattuna a taron?

Kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito, ana sa ran ƴan majalisa za su tattauna muhimman batutuwa da suka shafi ƙasa tare da tsohon shugaban.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sauran ‘yan majalisar da suka halarci taron sun hada da Hon. Peter Aniekwe, Hon. Matthew Nwogu, Hon. Abdulmaleek Danga, Hon. Midala Usman, da Hon. Kama Nkemkanma.

Da yake jawabi bayan fitowa daga taron, Obasanjo ya jaddada cewa Najeriya ba za je ko ina ba ta fannin ci gaba har sai shugabanni da talakawa sun gyara halayensu.

Obasanjo ya gargaɗi shugabanni

Ya yi gargadin cewa Najeriya na kan ƙaya wanda ka iya rugujewa da ita idan al’umma suka gaza daukar kwararan matakan da suka dace wajen magance dimbin kalubalen da ake fama da su.

Kamar yadda Punch ta ruwaito, Obasanjo ya bayyana Najeriya a matsayin kasar da ke tangal-tangal, tana kwan-gaba kwan-baya.

Kara karanta wannan

Matasa sun fusata da kisan ɗan uwansu, sun bankawa fadar basarake wuta a Arewa

Bugu da ƙari, tsohon shugaban kasar ya ce buƙatun masu zanga-zanga suna kan hanya kuma ya kamata gwamnati ta zauna da su ta saurare su.

Gwamna ya maida martani ga Tinubu

A wani rahoton kuma Gwamna Seyi Makinde ya musanta ikirarin Bola Ahmed Tinubu na rabawa jihohi N570bn domin ragewa al'umma raɗaɗin kuncin rayuwa

Tun farko shugaban ƙasa ya ce gwamnatinsa ta rabawa gwamnoni maƙudan kuɗi domin su faɗaɗa shirye-shiryen tallafawa ƴan Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262