Bola Tinubu Ya Shiga Taron FEC a Aso Villa Kwanaki 3 Gabanin Fara Zanga Zanga

Bola Tinubu Ya Shiga Taron FEC a Aso Villa Kwanaki 3 Gabanin Fara Zanga Zanga

  • Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci taron majalisar zartaswa kamar yadda aka saba a fadar shugaban kasa da ke babban birnin tarayya Abuja
  • Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima da sakataren gwamnatin tarayya sun halarci taron na ranar Litinin, 29 ga watan Yuli, 2024
  • Wannan taron na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin tarayya ke fuskantar zanga-zangar da ƴan Najeriya suka shirya yi a watan Agusta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na jagorantar taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) yanzu haka a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Idan ba ku manta ba a taron FEC da ya gabata, majalisar ta umarci ministan kasafin kudi da tsare-tsare Atiku Bagudu, ya lalubo matakan da za a bu don ckke giɓin kasafin 2024.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya rattaɓa hannu a dokar sabon mafi ƙarancin albashi, bayanai sun fito

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu.
Bola Tinubu ya shiga taron FEC a fadar shugaban kasa da ke Abuja Hoto: Ajuri Ngelale
Asali: Twitter

Kamar yadda The Nation ta ruwaito, majalisar ta ba ministan wannan umarni ne domin samo mafita kan gibin da da za a samu a kasafin kudin bayan aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Har ila yau a taron, gwamnatin tarayya ta umarci a tura tirelolin shinkafa 740 zuwa jihohi 36 da babban birnin tarayya Abuja domin a rabawa masu karamin karfi.

Manyan gwamnati sun halarci FEC

Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima da sakataren gwamnatin tarayya, George Akume sun halarci taron na yau Litinin, 29 ga watan Yuli, 2024.

Sauran kusoshin gwamnati da suka shiga zaman sun haɗa da shugaban ma'aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila da mai bada shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu.

Shugabar ma'aikatan gwamnatin tarayya da kusan duka ministoci da sauran mambobin FEC sun halarci taron yau a fadar shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan

Tinubu ya yi jawabi inda ya dawo da tallafin mai, wutar lantarki? gaskiya ta fito

Legit Hausa ta fahimci cewa wannan taron na zuwa ne kwanaki uku gabanin ranar da ƴan Najeriya suka shirya fara zanga-zanga kan tsadar rayuwa.

Gwamnatin Tinubu na tsoron zanga-zanga

Ana da labari cewa yayin da aka hango hadarin zanga-zanga, a gurguje aka amince da kudirin mafi karancin albashi da wasu dabaru.

Wasu suna alakanta tabbatar da yancin kananan hukumomi da daukar aikin da ake shirin yi a NNPC da yunkurin hana matasa zanga-zanga.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262