Tsohon Shugaban PDP Ya Fusata da Yadda Wasu Ke 'Satar' Kudi, Ya Fice Daga Jam'iyyar

Tsohon Shugaban PDP Ya Fusata da Yadda Wasu Ke 'Satar' Kudi, Ya Fice Daga Jam'iyyar

  • Tsohon shugaban PDP reshen jihar Ondo, Ebenezer Alabi ya sanar da ficewa daga jam'iyyar bisa wasu dalilai ana shirin zaɓen gwamna
  • Alabi ya bayyana cewa ba zai ci gaba da zama a jam'iyyar da jagororinta ba su da buri face su kwashe kuɗin kamfen da aka turo
  • Ya bayyana cewa ya yanke shawarar tattara kayansa ya bar PDP bayan tattaunawa da iyalai, ƴan uwa da abokan arziki

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Ondo - Rikicin cikin gida a babbar jam'iyyar adawa PDP reshen jihar Ondo ya buɗe sabon shafi a daidai lokacin da ake shirye-shiryen zaɓen gwamna a 2024.

Rahotanni sun bayyana tsohon shugaban PDP na jihar, Ebenezer Alabi, ya sanar da ficewa daga jam'iyyar.

Kara karanta wannan

Mataimakin gwamna ya tsokano rigima, ya faɗi gwamnan PDP da ya yi yunƙurin kashe shi

Umar Damagum.
Zaben Ondo: tsohon shugaban PDP a jihar Ondo, Ebenezer Alabi ya fice daga jam'iyyar Hoto: Ambassador Umar Damagun
Asali: Facebook

Mista Alabi ya riƙe kujerar shugaban jam'iyyar PDP a jihar Ondo a lokacin mulkin tsohon gwamna marigayi Olusegun Agagu, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa Alabi ya fice daga PDP?

Ya bayyana cewa ya yanke shawarin jefar da kwallon mangoro domin ya huta da ƙuda bayan tuntubar iyalansa, abokanan siyasa da abokanan arziƙi.

Ebenezer Alabi ya ce ba zai iya ci gaba da zama a jam'iyyar da jagororinta ba su da wani buri face su samu dama su tara kudi a lokacin zaɓen da ke tafe a jihar.

Hakan na ƙunshe ne a wasiƙar ficewa daga PDP da tsohon shugaban ya rubuta mai ɗauke da kwanan watan 18 ga Yuli, 2024.

A rahoton The Nation, Alabi ya ci gaba da cewa:

"Kuɗaɗen da aka turo domin kamfe a babban zaben da ya wuce sun kare ne a aljihunan waɗannan shugabanni waɗanda suka zama silar rashin nasarar PDP."

Kara karanta wannan

Gwamnan APC ya zama na farko a Arewa da ya amince zai fara biyan ma'aikata N70,000

Alabi ya ɗauki wannan mataki ne sa’o’i 24 bayan da wasu jiga-jigai da ‘ya’yan jam’iyyar PDP suka fice daga jam’iyyar adawa zuwa jam’iyyar APC mai mulki. 

APC ta mayar da martani ga PDP

Kuna da labarin jam'iyyar APC ta yi zazzafan martani ga PDP biyo bayan maganganu da gwamnonin jam'iyyar suka yi bayan kammala wani taro.

A jiya Alhamis, jami'in yada labaran APC, Barista Felix Morka ya yi martanin inda ya ce PDP ba ta da wani hurumin zarginsu a Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262