Fubara vs Wike: Gwamnonin PDP Sun Fadi Wanda Suke Goyon Baya a Rikicin Rivers

Fubara vs Wike: Gwamnonin PDP Sun Fadi Wanda Suke Goyon Baya a Rikicin Rivers

  • Gwamnonin jam'iyyar PDP sun nuna goyon bayansu ga gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara kan rikicin siyasar jihar
  • Ƙungiyar gwamnonin a cikin wata sanarwa sun bayyana cewa akwai ɓuƙatar masu ruwa da tsaki su shawo kan matsalar
  • Gwamna Siminalayi Fubara da magabacinsa Nyesom Wike sun koma ba su ga maciji da juna saboda rikicin siyasar jihar

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Enugu - Gwamnonin da aka zaɓa a ƙarƙashin jam'iyyar PDP sun bayyana goyon bayansu gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara.

Gwamnonin sun nuna goyon bayansu ga gwamnan ne kan rikicin siyasar jihar tsakaninsa da ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike.

Gwamnonin PDP sun goyi bayan Fubara
Gwamnonin PDP sun nuna goyon bayansu ga Gwamna Fubara Hoto: Sir Siminalayi Fubara, Nyesom Ezenwo Wike - CON
Asali: Facebook

Ƙungiyar gwamnonin na PDP sun bayyana goyon bayansu ga Gwamna Fubara ne a cikin wata sanarwa da suka fitar a ƙarshen taronsu a Enugu, cewar rahoton jaridar The Cable.

Kara karanta wannan

Gwamnonin PDP sun goyi bayan NLC, sun faɗi matsaya kan sabon mafi ƙarancin albashi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnonin sun bayyana cewa ya kamata a tattauna sosai da masu ruwa da tsaki domin samar da mafita kan rikicin siyasar da ke addabar jihar, rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

Rikicin Fubara da Wike ya ƙi ƙarewa

Goyon bayan na su dai na zuwa ne yayin da ake fama da rikicin siyasa a jihar mai arziƙin man fetur.

Gwamna Fubara na cikin rikicin siyasa da magabacinsa Nyesom Wike, wanda yanzu yake kan kujerar ministan birnin tarayya Abuja.

Rikicin siyasar ya sanya majalisar dokokin jihar Rivers ta rabe gida biyu inda wani ɓangare na goyon bayan Wike yayin da wani ɓangaren ke goyon bayan Gwamna Fubara.

Matsayar gwamnonin PDP kan rikicin Rivers

"Ƙungiyar ta lura da rikice-rikicen da ke faruwa a reshen jam'iyyar PDP na jihar Rivers kuma a shirye take wajen tabbatar da zaman lafiya."

Kara karanta wannan

PDP ta fadi lokacin kwace kujerun da ta rasa a hannun jam'iyyun siyasa, ta sha alwashi

"Ƙungiyar ta yanke shawarar goyon bayan gwamnan jihar Rivers, mai girma Siminalayi Fubara."

- Ƙungiyar gwamnonin PDP

Gwamnonin sun bayyana cewa ya kamata a tattauna sosai da masu ruwa da tsaki domin samar da mafita kan rikicin siyasar da ke addabar jihar.

Rikicin PDP ya ƙara ƙamari a Rivers

A wani labarin kuma, kun ji cewa rikicin jam’iyyar PDP a jihar Ribas ya kara kamari, biyo bayan hukuncin da wata kotu ta yanke na hana shugabannin jam’iyyar gudanar da babban taronta.

Babbar kotun da ke zamanta a Port Harcourt, babban birnin jihar, ta hana jam’iyyar gudanar da taron da ta shirya yi a ranar 27 ga watan Yulin 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng