Jerin Gwamnoni 13 da Suka Fara Gaggawar Shirya Zabe Bayan Hukuncin Kotun Ƙoli

Jerin Gwamnoni 13 da Suka Fara Gaggawar Shirya Zabe Bayan Hukuncin Kotun Ƙoli

Akalla gwamnoni 13 ne suka farga suka fara shirye-shiryen zaɓen kananan hukumomi a jihohinsu bayan hukuncin kotun ƙoli a Najeriya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Idan ba ku manta ba, kotu mai daraja ta ɗaya a Najeriya ta yanke cewa haramun ne gwamnoni su riƙa danne kuɗaɗen kananan hukumomi da aka turo daga tarayya

Gwamna Soludo, Siminalayi Fubara da Alia.
Gwamnoni sun fara hanzarin gudanar da zaben kananan hukumomi a jiohinsu Hoto: @CCSoludo, @SimFubaraƘSC, @Hyacinthalia
Asali: Twitter

Kotu ta ba kananan hukumomi 'yanci

Ta kuma bayyana cewa daga yanzu ƙanannan hukumomi 774 na da haƙƙi da ikon tafiyar da kason kuɗinsu, inda ta umarci a tura masu kudi kai tsaye.

Kotun ta yanke wannan hukuncin ne a ƙarar da Antoni Janar na kasa kuma ministan shari'a ya shigar da gwamnonin jihohi 36.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Har ila yau kotun ta bayyana cewa kantomomi da gwamnoni ke naɗawa sun saɓawa kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999, Punch ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Hukumar zaɓe ta sanar da ranar zaben ƙananan hukumomi a jihar Kaduna

Legit.ng ta tattaro muku gwamnonin da suka sanya ranar zaɓen kananan hukumomi bayan wannan hukunci, ga su kamar haka:

1. Uba Sani na Kaduna

Hukumar zaɓen Kaduna (KAD-SIECOM) ta sanar da cewa ranar 19 ga watan Oktoba, 2024 za ta gudanar da zaɓen kananan hukumomi a faɗin jihar.

Shugabannin kananan hukumomi da kansiloli a Kaduna sun shiga ofis ne a ranar 1 ga watan Nuwamba, 2021 kuma wa'adinsu zai ƙare ranar 31 ga watan Oktoba, 2024, rahoton Channels tv.

2. Ahmed Usman Ododo na jihar Kogi

Kamar dai Kaduna, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kogi ta sanar da cewa za ta gudanar da zaɓen kananan hukumomi ranar 19 ga watan Oktoba, 2024.

Shugaban hukumar, Mamman Eri ne ya bayyana haka a wurin taron masu ruwa da tsaki wanda ya gudana ranar Talata a birnin Lokoja.

Mamman ya bayyana cewa matakin ya yi daidai da tanadin kundin tsarin mulki wanda ya ɗora alhakin shirya zaɓen a wuyan hukumar.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Gwamnatin Kano ta sake bankado yadda Ganduje ya wawure dukiyar jihar

3. Bala Mohammed na Bauchi

Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ba a bar shi a baya ba yayin da hukumar zaɓen jihar ta zaɓi ranar 19 ga watan Agusta domin gudanar zaɓen ciyamomi da kansiloli.

Shugaban hukumar zaɓen Bauchi mai zaman kanta, Alhaji Ahmed Makama ne ya sanar da haka a wani taron manema labarai ranar Talata.

Ahmed Makama ya tabbatar da cewa sun yi dukkan shirye-shiryen da suka dace domin tabbatar da an gudanar da sahihin zaɓe.

4. Malam Dikko Radda na Katsina

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Katsina (KTSIEC) ta bayyana cewa za a gudanar da zaben kananan hukumomin jihar a ranar Asabar 15 ga Fabrairu, 2025.

Shugaban KTSIEC, Alhaji Lawal Alhassan Faskari, ya karfafa wa masu sha’awar tsayawa takara daga jam’iyyun siyasar da aka amince da su guiwarsu fito a fafata da su.

5. Gwamna Adeleke na jihar Osun

Hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Osun (OSIEC) ta bayyana cewa ba zata yi gaggawar gudanar da zaben kananan hukumomi ba duk da hukuncin kotun koli.

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP ya hango matsaloli a ƴancin kananan hukumomin Najeriya

A cewar shugaban OSIEC Hashim Abioye, hukumar tana nan a kan jadawalin zaben da ta fitar a baya wanda ta tsara yin zaɓen a watan Fabrairu, 2025, cewar The Nation.

Sauran gwamnonin sun haɗa da:

S/NJihaSunan gwamnaRanar zaɓe
6EnuguPeter Mbah5 ga watan Oktoba, 2024
7 BenuwaiHyacinth Alia16 ga watan Nuwamba, 2024
8RibasSiminalayi Fubara5 ga watan Oktoba, 2024
9JigawaUmar Namadi14 ga watan Yuni, 2024
10ImoHope UzodinmaWatan Satumba, 2024
11 KebbiDr. Nasir Idris31 ga watan Augusta, 2024
12Abia Alex OttiBabu takamaiman kwanan wata
13AnambraCharles SoludoBabu takamaiman kwanan wata

Gwamnan Eno ya yi maraba da hukuncin kotu

A wani rahoton kuma Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom ya ce bai taɓa ɗaukar ko sisi daga kason kuɗin da ake turo ma kananan hukumomin jihar ba.

Kara karanta wannan

Kotu ta tsige ɗan majalisar tarayya, ta umarci hukumar INEC ta shirya sabon zaɓe

Fasto Umo Eno ya yi maraba da hukuncin kotun koli na bai wa kananan hukumomi cikakken ƴancin karbar kason kudinsu daga tarayya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262