"Muna Maraba da Kai": Kwankwaso Ya Tura Sakon Gayyatar El Rufai Zuwa NNPP a Bidiyo

"Muna Maraba da Kai": Kwankwaso Ya Tura Sakon Gayyatar El Rufai Zuwa NNPP a Bidiyo

  • Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa jam'iyyar NNPP budaddiya ce ga kowa
  • Kwankwaso ya ce idan har tsohon gwamnan Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai yana son shigowa jam'iyyar to suna yi masa maraba da zuwa
  • Sanatan ya kuma bayyana amfanin sauya tambarin jam'iyyar da launinta bayan samun matsaloli a zaben shekarar 2023

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi magana kan bude kofa da suka yi ga duk mai son shiga jam'iyyar NNPP.

Kwankwaso ya ce suna maraba da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai idan zai shigo jam'iyyar.

Kwakwaso ya yi tayin shiga jam'iyyar NNPP ga El-Rufai
Rabi'u Kwankwaso ya ce suna maraba da El-Rufai idan zai shigo NNPP. Hoto: @KwankwasoRM.
Asali: Twitter

Kwankwaso ya yiwa El-Rufai tayin NNPP

Kara karanta wannan

Sabuwar tafiya: Hotunan yadda Kwankwaso ya kaddamar da sabon tambarin NNPP a Abuja

Tsohon gwamnan Kano ya bayyana haka ne a cikin wata hira a faifan bidiyo da BBC Hausa ta wallafa a shafin X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanatan ya ce jam'iyyar NNPP a bude take ga kowa da ke son shigowa har da tsohon gwamna, Mallam Nasiru El-Rufai.

Kwankwaso ya kuma bayyana dalilin sauya tambarin jam'iyyar inda ya ce sun ci karo da matsaloli a zaben 2023.

"Ita jam'iyya a bude take, Malam Nasiru El-Rufai idan zai shigo muna yi masa maraba da zuwa."
"Haka kuma kowane ɗan Najeriya yana da dama ya shigo jam'iyyar kamar yadda yake da damar fita."

- Rabi'u Kwankwaso

"Musabbabin sauya tambarin NNPP" - Kwankwaso

Ya ce babu kamshin gaskiya kan zargin wai rikicin cikin gida ne musabbabin sauya tambarin jam'iyyar.

Sanatan ya ce musabbabin bai rasa nasaba da matsalolin da suka fuskanta wurin gane jam'iyyar a takardar kuri'a a zabe.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya faɗi jihar da za ta fara amfani da sabon tambarin NNPP a Najeriya

Kwankwaso ya magantu kan korarsa a NNPP

A wani labarin, kun ji cewa jagoran jam'iyyar NNPP a Najeriya, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce har yanzu su ne halastattun ƴan jam'iyyar.

Sanata Kwankwaso ya ce kuma sun koma jam'iyyar domin samar da kyakkyawar manufa ta ceto Najeriya da ƴan ƙasar.

Ya bayyana cewa babu wanda ke da ikon korarsa daga jam’iyyar da suka raya har ta kai ga matakin da ta ke a yanzu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.