Ganduje Ya Ga Ta Kansa, Wasu Manyan Jiga Jigai da Mambobin APC Sun Koma PDP
- Yayin da ake shirin zaben gwamna a jihar Ondo, wasu jiga-jigai da mambobin APC sama da 1000 sun sauya sheka zuwa jam'iyyar adawa PDP
- Masu sauya shekar sun bayyana cewa sun baro APC ne saboda rigingimun cikin gida da kuma kudirinsu na kawar da jam'iyyar da ta kawo 'yunwa'
- Sun kuma sha alwashin cewa za su marawa ɗan takarar gwamna a inuwar PDP baya a zaɓen da za a yi ranar 16 ga watan Nuwamba
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Ondo - 'Ya 'yan jam'iyyar APC mai mulki fiye da 1000 a ƙaramar hukumar Akure ta Kudu sun sauya sheƙa zuwa PDP jihar Ondo.
Masu sauya sheƙar karkashin jagorancin Mayowa Ajemoju Boboye sun bayyana rashin bai wa kowa haƙƙinsa a matsayin dalilin barin APC mai mulki.

Kara karanta wannan
Ana tsaka da rigimar sarautar Kano, kotu ta ɗauki mataki a shari'ar tsige Ganduje

Source: Facebook
An fice daga jam'iyyar APC
Daga cikin wadanda suka sauya sheka akwai shugaban jam’iyyar APC na gunduma ta 8, Deborah Owosusi da Ademola Ayonijebul, The Nation ta rahoto.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sauran jiga-jigan da ke cikin tawagar masu sauya shekar sun haɗa da Mayowa Boboye, Oloro Alejo, da Azeez Ibrahim wanda ya jagoranci tawagar ƴan Ebira.
Ondo: An sha alwashin karya APC
Sun yi alkawarin goyon bayan PDP da dan takararta na gwamna Hon Agboola Ajayi a zaben gwamnan da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba.
A cewarsu za su yi duk mai yiwuwa wajen kawar da jam’iyya mai mulki daga gidan gwamnatin Ondo a zaɓe mai zuwa.
Yadda PDP ta yi masu maraba
Jam'iyyar PDP ta tarbi tsofaffin 'ya 'yan na jam’iyyar APC ne a wani taro da ta shirya ma musamman a babban dakin taro da ke birnin Akure, Vanguard ta ruwaito.

Kara karanta wannan
IPMAN: Farashin litar man fetur ya kai N2,000 a jihar Arewa, an gano dalilin tashin
Da yake magana a madadin wadanda suka sauya sheka, tsohon sakataren APC a Akure ta Kudu, Akinwande Fayinminu, ya soki shugabannin APC, inda ya zarge su da kawo yunwa a ƙasa.
"APC ta rasa zaman lafiya da adalci a cikin gida shiyasa kuka ga kawunansu sun rabu, ba za mu iya zama a ciki ba," in ji shi.
Fubara ya zargi mutanen Wike da ta'adi
A wani rahoton kuma Gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara ya zargi mutanen Nyesom Wike da hannu a kokarin tashin bam a birnin Fatakwal.
Fubara ya bayyana cewa an shirya tayar da bam ne domin a jawo hankalin gwamnatin tarayya ta ayyana dokar ta ɓaci a Ribas.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng