Ganduje Ya Ga Ta Kansa, Wasu Manyan Jiga Jigai da Mambobin APC Sun Koma PDP

Ganduje Ya Ga Ta Kansa, Wasu Manyan Jiga Jigai da Mambobin APC Sun Koma PDP

  • Yayin da ake shirin zaben gwamna a jihar Ondo, wasu jiga-jigai da mambobin APC sama da 1000 sun sauya sheka zuwa jam'iyyar adawa PDP
  • Masu sauya shekar sun bayyana cewa sun baro APC ne saboda rigingimun cikin gida da kuma kudirinsu na kawar da jam'iyyar da ta kawo 'yunwa'
  • Sun kuma sha alwashin cewa za su marawa ɗan takarar gwamna a inuwar PDP baya a zaɓen da za a yi ranar 16 ga watan Nuwamba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Ondo - 'Ya 'yan jam'iyyar APC mai mulki fiye da 1000 a ƙaramar hukumar Akure ta Kudu sun sauya sheƙa zuwa PDP jihar Ondo.

Masu sauya sheƙar karkashin jagorancin Mayowa Ajemoju Boboye sun bayyana rashin bai wa kowa haƙƙinsa a matsayin dalilin barin APC mai mulki.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da rigimar sarautar Kano, kotu ta ɗauki mataki a shari'ar tsige Ganduje

Umar Damagun da Ganduje.
PDP ta samu ƙarin goyon baya yayin da ake shirin zaben gwamna a jihar Ondo Hoto: Umar Damagum, Dr. Abdullahi Umar Ganduje
Asali: Facebook

An fice daga jam'iyyar APC

Daga cikin wadanda suka sauya sheka akwai shugaban jam’iyyar APC na gunduma ta 8, Deborah Owosusi da Ademola Ayonijebul, The Nation ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sauran jiga-jigan da ke cikin tawagar masu sauya shekar sun haɗa da Mayowa Boboye, Oloro Alejo, da Azeez Ibrahim wanda ya jagoranci tawagar ƴan Ebira.

Ondo: An sha alwashin karya APC

Sun yi alkawarin goyon bayan PDP da dan takararta na gwamna Hon Agboola Ajayi a zaben gwamnan da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba.

A cewarsu za su yi duk mai yiwuwa wajen kawar da jam’iyya mai mulki daga gidan gwamnatin Ondo a zaɓe mai zuwa.

Yadda PDP ta yi masu maraba

Jam'iyyar PDP ta tarbi tsofaffin 'ya 'yan na jam’iyyar APC ne a wani taro da ta shirya ma musamman a babban dakin taro da ke birnin Akure, Vanguard ta ruwaito.

Kara karanta wannan

IPMAN: Farashin litar man fetur ya kai N2,000 a jihar Arewa, an gano dalilin tashin

Da yake magana a madadin wadanda suka sauya sheka, tsohon sakataren APC a Akure ta Kudu, Akinwande Fayinminu, ya soki shugabannin APC, inda ya zarge su da kawo yunwa a ƙasa.

"APC ta rasa zaman lafiya da adalci a cikin gida shiyasa kuka ga kawunansu sun rabu, ba za mu iya zama a ciki ba," in ji shi.

Fubara ya zargi mutanen Wike da ta'adi

A wani rahoton kuma Gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara ya zargi mutanen Nyesom Wike da hannu a kokarin tashin bam a birnin Fatakwal.

Fubara ya bayyana cewa an shirya tayar da bam ne domin a jawo hankalin gwamnatin tarayya ta ayyana dokar ta ɓaci a Ribas.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262