“Siddabarun Siyasa Ne”: Na Hannun Daman Atiku Ya Fadi Dalilin Ziyartar Buhari

“Siddabarun Siyasa Ne”: Na Hannun Daman Atiku Ya Fadi Dalilin Ziyartar Buhari

  • Tsohon dan takarar shugaban kasa a 2023, Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari a jihar Katsina
  • Atiku ya kai ziyarar ne domin gaisuwar salla ga tsohon shugaban kasa a gidansa da ke Daura a jiya Asabar 22 ga watan Yunin 2024
  • Masu fashin baki da dama sun yi ta magana kan dalilin ziyarar, sai dai na hannun daman Atiku ya ce duk maganar zaben 2027 ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Katsina - Na hannun daman Atiku Abubakar ta bayyana dalilin ziyarar dan takarar ga Muhammadu Buhari a Katsina.

Dan jam'iyyar PDP ya ce ganawar ba ta rasa nasaba da shirye-shiryen zaben 2027 da ake tunkara a nan gaba kadan.

Kara karanta wannan

Matsin rayuwa: Tinubu ya shawarci 'yan Najeriya kan yadda za su samu abinci cikin sauki

Musabbin ziyarar Atiku ga Buhari a Katsina
An tabbatar da abin da Atiku da Buhari suka tattauna a Katsina. Hoto: @Atiku.
Asali: Twitter

Atiku ya ziyarci Buhari a Katsina

Majiyar da ta bukaci boye sunanta ta bayyanawa Daily Trust cewa tattaunawar ta kuma kunshi halin da kasar ke ciki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Har ila yau, duk da sun samu sabani a wasu bangarori amma sun tattauna sosai kan zaben da ake tunkara a 2027, Legit ta tattaro.

"Abin da zan iya fada shi ne akwai hikima a ziyarar, ba zan baku cikakkaen bayani ba, amma sun tattauna halin da kasa rke ciki."
"Daga cikin tattaunawar akwai zaben 2023 da kuma zaben 2027 da ake tunkara, ba wai sun tsayar da matsaya ba ne saboda ka san ba wai suna kusanci ba ne."

- Cewar majiyar

Atiku ya magantu kan rikicin PDP

Har ila yau, a ranar Asabar, 22 ga watan Yunin 2024 dan takarar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya bayyana matsayarsa dangane da rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP.

Kara karanta wannan

Zaben 2027: Atiku ya bayyana mafita 1 game da rikicin da ya mamaye PDP a Katsina

Atiku ya kuma ziyarci Gwamna Dikko Umaru Radda yayin bayan ziyarartar Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura a Nijar.

Atiku ya ziyarci Buhar a Katsina

A wani labarin, kun ji cewa Dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya ziyarci Muhammadu Buhari.

Atiku ya kai ziyarar domin gaisuwar sallah ga tsohon shugaban kasar da suka fafata a zaben 2019 da kuma 2023.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya samu rakiyar tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel