Hotuna da Bidiyo: Mata Sun Ɓarke da Zanga-Zanga a Hedkwatar APC Ta Ƙasa

Hotuna da Bidiyo: Mata Sun Ɓarke da Zanga-Zanga a Hedkwatar APC Ta Ƙasa

  • Wasu fusatattun mambobin jam'iyyar APC mata sun mamaye hedkwatar jam'iyyar da ke birnin tarayya Abuja ranar Jumu'a
  • Dandazon matan sun gudanar da zanga-zanga ne domin nuna rashin jin daɗinsu da halin shugabar matan APC Mary Alile-Idele
  • Legit Hausa ta gano cewa matan da suka yi wannan zanga-zanga karkashin ƙungiyar mata masu kishi, sun nemi Alile Idele ta yi murabus

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Wasu gungun mata da suka fito zanga-zanga sun mamaye hedikwatar jam’iyyar APC mai mulki a Abuja ranar Juma’a, 31 ga watan Mayu.

Dandazon matan sun buƙaci shugabar matan jam'iyyar APC ta ƙasa, Mary Alile-Idele ta yi murabus daga kan muƙaminta.

Zanga-zangar matan APC.
Mambobin APC mata sun buƙaci shugabar matan jam'iyyar ta ƙasa ta yi murabus Hoto: @AllAroungNGR
Asali: Twitter

Suna zargin Alile-Idele da rashin kulawa da mambobi mata a APC, sannan tana amfani da kujerarta wajen cika wani burinta na ƙashin kai.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da rikicin sarautar Kano, jam'iyyar Kwankwaso ta aike da saƙo ga Bola Tinubu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito, zanga-zangar ta gudana ne karkashin jagorancin Rebecca Sheneni, kodinetar ƙungiyar mata masu kishin APC.

Meyasa matan APC ke zanga-zanga?

Yayin da take hira da ƴan jarida, shugabar masu zanga-zanga ta ce maimakon ta maida hankali wajen kula da matan APC, shugabar matan jam'iya ta koma tallata kasuwancinta.

"Mun damu matuka ganin yadda tun da ta shiga ofis, Misis Mary Alile-Idele ta nuna rashin kwarewa, alamu sun nuna kasuwancinta ta sa a gaba ba jam'iyyar APC ba.
"Muna da shaidar yadda take yawo zuwa jihohi domin rantsar da shugabannin ƙungiyarta mai zaman kanta (NGO) maimakon a ganta tana tallata manufofin APC ga mata."
“Duba da ɗimbin kuskurenta da rashin da’a, muna kira da a gaggauta tsige ta daga jam’iyyar APC. Ta nuna ba za ta iya ba kuma mu mun gaji haka nan."

Kara karanta wannan

Shugabancin APC: Kotu ta sanya ranar fara sauraron karar neman tsige Ganduje

Shugabar matan Imo ta kare Alile-Idele

Sai dai Misis Patricia Okuebor-Benson, shugabar matan APC ta jihar Imo, ta shiga sahun masu kare Alile-Idele, inda ta ce zargin ba gaskiya ba ne.

“Ba mu san daga ina waɗannan matan suke samun labaransu ba. Ina ganin wani ne ke daukar nauyinsu."

Za a fara sauraron ƙarar Ganduje

A wani rahoton kuma babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja ta tsayar da ranar da za ta fara sauraron ƙarar da aka shigar kan Abdullahi Umar Ganduje.

Alƙalin kotun mai shari'a Inyang Ekwo ya sanya ranar, 13 ga watan Yuni domin fara sauraron ƙarar wacce ke neman a tsige Ganduje daga shugabancin APC.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel