"Kano Ta Kama Hanyar Kamawa da Wuta," Jigo Ya Buƙaci Tinubu Ya Dakatar da Gwamna Abba

"Kano Ta Kama Hanyar Kamawa da Wuta," Jigo Ya Buƙaci Tinubu Ya Dakatar da Gwamna Abba

  • Ɗanbalki Kwamanda ya yi kira ga Bola Tinubu ya sa baki a rikicin sarautar Kano tun kafin gwamnati ta kafa tarihi mara kyau
  • Ya ce jihar Kano ta kama hanyar kamawa da wutar rikici matukar shugaban ƙasa bai gaggauta taka wa abin birki ba
  • Ɗan siyasar ya ce yana mamakin yadda Abba Yusuf ya sa ƙafa ya shure umarnin kotu ya manta cewa kotu ce ta tabbatar masa da nasara

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Alhaji Abdulmajid Danbilki-Kwamanda ya yi kira ga shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya takawa Gwamna Abba Kabir Yusuf birki.

Danbilki Kwamanda ya bukaci Tinubu ya dakatar da gwamnatin Kano tun kafin ta kafa mummunan tarihi a zamanin mulkinsa.

Bola Tinubu da Abba.
Danbalki Kwamanda ya bukaci Bola Tinubu ya sa aki a rikicin sarautar Kano Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Abba Kabir Yusuf
Asali: Twitter

Sanusi II: Danbilki ya taso gwamna Abba

Abokin siyasar na tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, Danbilki Kwamanda ya faɗi haka ne yayin zantawa da menama labarai kan rikicin sarautar Kano ranar Talata.

Kara karanta wannan

Rikicin Kano: Abin da Sarki Sanusi II ya faɗawa manyan jami'an tsaro a fadarsa

Ya gargaɗi shugaba Tinubu kar ya bari gwamnatin Kano ta fake da wasu dokokin jihar wajen saɓa umarnin kotu da ta hana mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin sarkin Kano.

An take doka wajen nada Sarkin Kano?

A cewarsa, abin da gwamnatin Kano ta aikata ya ci karo da umarnin babbar kotun tarayya, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

A kalamansa ya ce:

"Abin da gwamnatin Kano ke yi ya saɓawa umarnin babbar kotun tarayya wanda ta hana dawo da Muhammadu Sanusi II, tana kokarin kafa mummunan tarihin da zai shafi kowa.
"Na kasa fahimtar yadda gwamnatin da kotu ta kafa, a yanzu ta dawo tana neman sa ƙafar wando ɗaya da umarnin kotun wacce ke ƙoƙarin hana ta aikata kuskure.
"Mu ajiye siyasa a gefe, ƙoƙarin ƙaƙaba sabon sarkin da aka dawo da shi a matsayin shi ne sahihin sarkin Kano barazana ce ga kundin tsarin mulki da zaman lafiya."

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta dakatar da muhimmin aikin da Buhari ya fara a Najeriya

Kano: Ya kamata Tinubu ya sa baki

Ɗanbalki Kwamanda ya buƙaci shugaban ƙasa ya gaggauta sa baki kan rikicin da ke faruwa domin dawo da zaman lafiya a jihar Kano, cewar Daily Post.

“Muna kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya gaggauta yin abin da ya dace ya tsoma baki a cikin lamarin domin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar," in ji shi.

Yan sanda sun shirya tsaf a Kano

A wani rahoton kuma, an ji yan sanda sun shirya ɗaukar matakai masu tsauri kan duk wanda ya yi ƙoƙarin tayar da fitina a jihar Kano yayin da ake taƙaddamar sarauta

CP Usaini Gumel, kwamshinan ƴan sandan jihar ya ce ba za su lamunci wasu tsiraru su ruguza zaman lafiyar da ake da ita a Kano ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel