Gwamnan PDP Ya Naɗa Kwamishinoni 2 Bayan Watanni 8 a Kan Mulki, Ya Aike da Saƙo Majalisa

Gwamnan PDP Ya Naɗa Kwamishinoni 2 Bayan Watanni 8 a Kan Mulki, Ya Aike da Saƙo Majalisa

  • Gwamna Oborevwori na jihar Delta ya naɗa sabbin kwamishinoni 2 bayan hawa mulki watanni takwas da suka wuce
  • Rahoto ya nuna tun da gwamnan ya ɗare madafun iko, wannan ne na farko da ya naɗa kwamishinan yaɗa labarai da kwamishinan shari'a
  • Majalisar dokokin jihar Delta ta karɓi sunayen waɗanda aka naɗa kuma ta sanya ranar tantance su a makon gobe

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Jihar Delta - Bayan shafe sama da watanni takwas a kan madafun iko, Gwamna Sherrif Oborevwori ya naɗa kwamishinoni biyu da aka jima ana jira a jihar Delta.

Gwamnan na jam'iyyar PDP ya sanar da sunayen mutum biyu da ya naɗa a matsayin kwamishinan yaɗa labarai da Antoni Janar kuma kwamishinan shari'a.

Gwamna Sherrif Oborevwori na jihar Delta.
Gwamna Oborevwori Ya Nada Kwamishinoni 2 Bayan Shafe Watanni 8 a Mulkin Delta Hoto: Sherrif Oborevwori
Asali: Facebook

Jerin sabbin kwamishinonin da Oborevwori ya naɗa

Wadanda gwamnan ya naɗa sun haɗa da sakataren watsa labaran jam'iyyar PDP reshen Delta, Dakta Ifeanyi Osuoza, a matsayin kwamishinan yaɗa labarai.

Kara karanta wannan

Kano: An aike da babban saƙo ga Gwamna Abba kan kwamishinan da ya yi wa alƙalai barazanar kisa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai kuma Ekemejero Ohwovoriole, babban lauya a Najeriya da ya kai matakin SAN a matsayin Antoni Janar kuma kwamishinan shari'a na jihar Delta, Tribune ta tattaro.

Har ila yau, gwamnan ya sanar da nadin tsohon shugaban karamar hukumar Bomadi, Kalanama Penawou, a matsayin kwamishinan kananan hukumomi da masarautu.

Gwamna ya aika sunayensu ga majalisar dokokin jihar

Gwamna Oborevwori ya aika da sunayen waɗannan kwamishinoni da ya naɗa zuwa majalisar dokokin jihar ranar Talata, 23 ga watan Janairu, 2024.

Kakakin majalisar dokokin, Rt. Honorabul Emomotimi Guwor, ya karanta sunayen mutanen a zauren majalisar yayin zamansu na jiya Talata.

Ana sa ran kowane daga cikin wadanda aka nada zai mika kwafi 35 na kundin bayanan karatunsa (CV) ga magatakardar majalisar daga nan zuwa ranar Litinin mai zuwa.

Sannan kuma zasu bayyana a gaban majalisar domin tantnace su a makon gobe ranar Talata, 30 ga watan Janairu, 2024.

Kara karanta wannan

Gwamnan arewa ya haramta amfani da kowane kalar babur, ya kafa doka kan amfani da Keke Napep

An dakatar da biyan wasu ma'aikata albashi a Kogi

A wani rahoton na daban Gwamnatin Yahaya Bello na jihar Kogi ta dakatar da biyan albashin ma'aikata 231 tun watan Nuwamban, 2023.

Shugabar ma'aikatan jihar, Hannah Odiyo, ta ce an ɗauki wannan matakin ne saboda ma'aikatan sun taka umarnin gwamnati.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262