Kano: Jami'yyar APC Ta Yi Martani Kan Kiran Tinubu Ya Kori Ganduje, Ta Tona Asirin Kwankwasiyya
- Jami'yyar adawa ta APC a jihar Kano ta yi martani kan kiraye-kirayen korar shugaban jam'iyyar ta kasa, Dakta Abdullahi Ganduje
- Mataimakin shugaban jam'iyyar a jihar, Shehu Maigari ya yi fatali da kiraye-kirayen inda ya ce 'yan Kwankwasiyya ne suka dauki nauyinsu
- Wannan na zuwa ne bayan wasu matasan jam'iyyar APC sun bukaci Tinubu ya kori Ganduje bayan gaza yin nasara a zaben gwamnan jihar
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Kano - Jami'yyar APC a jihar Kano ta yi zazzafan martani kan kiran a kori shugaban jam'iyyar, Umar Ganduje.
Jami'yyar adawa a jihar ta ce 'yan Kwankwasiyya ne suka dauki nauyin matasan APC kan wannan kira da a sauke Ganduje.

Kara karanta wannan
Kano: Dattawan APC a jihar sun shawarci Tinubu kan korar Ganduje, sun bayyana matsayarsu

Asali: Facebook
Wane kira matasan suka yi kan korar Ganduje?
Idan ba a mantaba a jiya Lahadi 21 ga watan Janairu wata kungiyar matasa ta bukaci Tinubu ya kori Ganduje daga kan kujerar shugabancin jam'iyyar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Matasan sun yi wannan kira ne yayin da suke zargin Ganduje da gaza yin nasara a zaben jihar da aka gudanar a watan Maris.
Shugaban kungiyar, Sadiq Ali Sango shi ya yi wannan kira a jiya Lahadi 21 ga watan Janairu a Kano, kamar yadda The Guardian ta tattaro.
Wane martani APC ta yi kan korar Ganduje?
Mataimakin shugaban jam'iyyar a jihar, Shehu Maigari ya yi fatali da kiran inda ya ce matasan ba 'yan APC ba ne.
Maigari ya ce sun sani a APC ba su da matasan da ke kiran haka, kuma shugabanninta sun san masu daukar nauyin irin wadannan, cewar Daily Trust.

Kara karanta wannan
A je a sasanta da Kwankwaso: Sirrin taron Ganduje, ‘yan APC da Tinubu sun fito fili
Wannan na zuwa ne yayin da ake zargin akwai wani shirin hadaka tsakanin Sanata Kwankwaso da jami'yyar APC.
Jita-jitar komawar Kwankwaso APC
Kun ji cewa, Jita-jitar komawar Sanata Rabiu Kwankwaso ta kara tabbata bayan ganinsa da jigon APC, Cif Bisi Akande.
A baya, ana ta rade-radin cewa Sanatan ya yi yarjejeniya da jam'iyyar APC cewa akwai alamun ya koma jam'iyyar inda shi kuma a bangarensa ya musanta zargin.
Wannan na zuwa ne bayan samun nasara a Kotun Koli da Gwamna Abba Kabir ya yi wanda ya kasance dan jam'iyyar NNPP.
Asali: Legit.ng