Kotun Koli Ta Sake Yanke Hukuncin Karshe Kan Shari'ar Neman Kifar da Gwamnan Kebbi

Kotun Koli Ta Sake Yanke Hukuncin Karshe Kan Shari'ar Neman Kifar da Gwamnan Kebbi

  • Kotun Koli ta yanke hukuncin karshe kan takaddamar zaben gwamnan jihar Kebbi a Arewacin Najeriya
  • Kotun ta tabbatar da nasarar Gwamna Nasir Idris na jam'iyyar APC a matsayin halastaccen gwamnan jihar
  • Kotun kuma har ila yau, ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Aminu Bande saboda rashin hujjoji

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kotun Koli ta yi hukunci kan takaddamar shari'ar zaben gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris.

Kotun ta tabbatar da nasarar Gwamna Nasir Idris na jam'iyyar APC a matsayin halastaccen gwamnan jihar, cewar Channels TV.

Kotun Koli ta yi hukunci kan shari'ar zaben gwamnan Kebbi
Kotun Koli ta tabbatar da nasarar Gwamna Nasir Idris a matsayin gwamna. Hoto: Nasir Idris.
Source: Facebook

Wane hukunci kotun ta yanke kan shari'ar Kebbi?

Har ila yau, kotun ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Aminu Bande saboda rashin gamsassun hujjoji.

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta yi hukuncin karshe a shari'ar neman tumbuke gwamnan Gombe, ta fadi dalillai

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yayin hukuncin, dukkan alkalan kotun sun amince da cewa korafe-korafen dan takarar PDP ba su da tasiri kamar yadda Kotun Daukaka Kara ta yi hukunci.

A baya, Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Nasir Idris na APC a matsayin zababben gwamnan jihar.

Yayin da kuma ta yi watsi da karar Bande wanda ya yi takara a jam'iyyar PDP a zaben na watan Maris, cewar The Nation.

Sauran hukunce-hukuncen da Kotun Koli

Tun farko, Hukumar zabe mai zaman kanta, INEC ta tabbatar da nasarar Gwamna Nasir Idris a matsayin wanda ya lashe zaben.

Aminu Bande a bangarensa, ya kalubalanci zaben da aka gudanar a watan Maris da cewa akwai kura-kurai cike a ciki.

Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da sauraran shari'ar zabukan jihohi da dama a Kotun Koli da ke Abuja.

Kotun Koli ta yi hukunci a zaben jihar Gombe

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta yanke hukuncin karshe kan shari'ar neman tsige gwamnan APC, akwai dalilai

Kun ji cewa Kotun Koli ta yi hukunci kan shari'ar zaben gwamnan jihar Gombe a yau Juma'a.

Kotun ta tabbatar da nasarar Gwamna Inuwa Yahaya na jami'yyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar.

Yayin da ta yi watsi da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP a zaben, Jibrin Barde saboda rashin gamsassun hujjoji.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.