Kai Tsaye: Shari'ar Zaben Gwamnonin Jihohin Bauchi da Zamfara Ke Gudana
Kotu ta tabbatar da nasarar Mohammed matsayin gwamnan Bauchi
Rahotan da Legit Hausa ke samu yanzu na nuni da cewa Kotun Koli ta tabbatar da nasarar zaben Bala Mohammed matsayin gwamnan jihar Bauchi, rahoton The Cable.
Kotun ta yi watsi da ƙarar da APC da dan takararta Sadique Abubakar suka shigar na kalubalantar hukuncin Kotun Daukaka Kara da na kotun sauraron kararrakin zaben jihar
An fara sauraran shari'ar zaben jihar Bauchi
Bayan yanke hukunci kan shari'ar gwamnan jihar Legas, Kotun Koli ta fara karanta shari'ar gwamnan Bauchi.
Jam'iyyar APC da dan takarar ta Sadique Abubakar ne suka shigar da karar, inda suke so kotun ta ruguza zen jihar da ya ba Gwamna Bala Mohammed nasara.Bayan yanke hukunci kan shari'ar gwamnan jihar Legas, Kotun Koli ta fara karanta shari'ar gwamnan Bauchi. Jam'iyyar APC da dan takarar ta Sadique Abubakar ne suka shigar da karar, inda suke so kotun ta ruguza zen jihar da ya ba Gwamna Bala Mohammed nasara. Bayan yanke hukunci kan shari'ar gwamnan jihar Legas, Kotun Koli ta fara karanta shari'ar gwamnan Bauchi. Jam'iyyar APC da dan takarar ta Sadique Abubakar ne suka shigar da karar, inda suke so kotun ta ruguza zen jihar da ya ba Gwamna Bala Mohammed nasara.