Wata Sabuwa: Na Hannun Damar Wike Ya Yi Murabus Daga Matsayin Shugaban Ma’aikatan Fubara
- Shugaban maika'atan Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas, Chidi Amadi ya sauka daga kan kujerarsa
- Amadi wanda ya kasance mai biyayya ga ministan Abuja, Nyesom Wike, ya yi murabus daga kujerarsa ne a daidai lokacin da rikicin siyasar da ya dabaibaye jihar ya ki ci ya ki cinyewa
- Da yake tabbatar da ci gaban, kwamishinan labarai da sadarwa na jihar Ribas, Joseph Johnson, ya ce Gwamna Fubara zai sanar da madadinsa a lokacin da ya kamata
Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum
Port Harcourt, Jihar Rivers - Chidi Amadi, Shugaban maika'atan Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas, ya yi murabus daga kan kujerarsa.
Kamar yadda jaridar Punch ta rahoto a safiyar Alhamis, 11 ga watan Janairu, kwamishinan labarai da sadarwa na jihar Ribas, Joseph Johnson, ya tabbatar da murabus din Amadi.

Kara karanta wannan
Shehu Sani ya yi shagube ga Betta kan alkawarinta na fitar da yan Najeriya miliyan 50 daga talauci

Asali: Twitter
Rikicin Ribas: Chidi Amadi ya yi murabus
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da aka shafe tsawon watanni ana rikicin siyasa a jihar da jam'iyyar PDP ke iko a cikinta.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Johnson ya ce Gwamna Fubara zai sanar da wanda zai maye gurbin Amadi, wanda ya kasance mai biyayya ga tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike, a lokacin da ya dace.
Ya ce:
"Tsohon shugaban ma'aikata, Honb Chidi Amadi, ya yi murabus. Gwamnan zai sanar da sabon shugaban ma'aikata a lokacin da ya dace.
“Hakkin gwamna ne ya nada mukami a lokacin da ya so. Zai gaya mana kuma za mu sanar da ku kuma za ku sami sanarwa a kan haka."
Wike ya aika sakon gargadi ga Fubara
A baya mun ji cewa Ministan Abuja, Nyesom Wike ya tura sakon gargadi ga Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Rivers. Wike ya bayyana cewa a yanzu ba lokacin siyasa ba ne amma idan lokacin ya yi za a gane waye ne a sama.

Kara karanta wannan
Ministan Abuja Wike ya yi kicibis da abokin karatunsa na sakanbdare, ya yi masa kyautar kudi a bidiyo
Ministan ya bayyana haka ne a ranar Asabar 6 ga watan Disamba yayin ganawa da tsohon amininsa a siyasa, Cif Victor Giadom.
Ya ce bai damu da dukkan zage-zagen da ake yi a kafofin yada labarai ba inda ya ce ba a zabe a kafar sadarwa, cewar Vanguard.
Asali: Legit.ng