Tsohon Gwamna Ya Fadi Hakikanin Halin da Buhari Ya Damkawa Tinubu Asusun Najeriya

Tsohon Gwamna Ya Fadi Hakikanin Halin da Buhari Ya Damkawa Tinubu Asusun Najeriya

  • Cif Olusegun Osoba ya ce da aka canza gwamnatin tarayya, sai aka samu baitul-mali babu komai a cikinsa
  • ‘Dan siyasar ya ce ya zama dole Bola Ahmed Tinubu ya ci bashin kudi akalla har zuwa bayan shekara guda
  • A lokacin da Muhammadu Buhari ya bar Aso Rock, wasu suna zargin an yi kaca-kaca da tattalin arzikin kasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ogun - Dattijo kuma tsohon gwamna a jihar Ogun, Olusegun Osoba ya ce babu abin da Bola Ahmed Tinubu ya samu cikin baitul-mali.

A wata hira da aka yi da shi a tashar Arise a makon nan, Cif Olusegun Osoba ya tofa albarkacin bakinsa kan irin halin da ake ciki.

Buhari-Tinubu
Bola Tinubu ya gaji Muhammadu Buhari Hoto: @Dolusegun, @MBuhari
Asali: Twitter

Tun kafin Muhammadu Buhari ya bar ofis a Mayun 2023, ‘dan siyasar ya ce ana cikin kalubale ta fuskar tattalin arziki a Najeriya.

Kara karanta wannan

"Sun ce zai kammalu a Disamba": Iyali sun kadu bayan ganin katafaren gidansu a kauye

Bola Tinubu zai kawo sauki a 2024?

Tsohon gwamnan ya ce Mai girma Bola Tinubu yana bakin kokarinsa wajen ganin ya kawar da wahalhalun da al’ummarsa ke sha.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun da aikin gama ya gama, This Day ta ce Segun Osoba ya ce sai da a sa ran abubuwa za su gyaru cikin 2024 da aka shiga.

Osoba ya ce dole Tinubu ya ci bashi

"An yi wa baitul-mali wayam, tsohuwar gwamnati tana cin bashi domin biyan albashi, kusan babu komai a ko ina.
Meya rage ayi a lokacin in ban da a ci bashi domin a cike gibin?
Hakan bai nufin a cigaba da al’adar cin bashi har abada. Bayan shekarar farko a ofis, za a sake dubawa a ga ya za ayi.

- Segun Osoba

Saura kiris abubuwa su ruguje a Najeriya

Kara karanta wannan

A Jawabin Shiga 2024, Shugaba Tinubu Ya Bayyana Ministoci da Hadiman da Zai Kora

Na yi maku bayani cewa mun yi sa’a, amma zuwa 1 ga watan Yuni, an shirya komai zai ruguje gaba daya.
Ina fada maku idan ba don shi (Tinubu) ya dauki hanyar da gwamnati ta dauka ba, da komai ya ruguje.

- Segun Osoba

Laifin Muhammadu Buhari ne ko kuwa?

Da Punch ta yi hira da Adebayo Folorunsho Francis kwanaki, ya fadi irin hakan, ya ce Muhammadu Buhari ya bar baya da kura a kasar.

Tsohon shugaban na APC a Legas ya ce tun ba yau ba tattalin arziki ya ruguje, ya kuma ce haka abin yake har a wasu kasashen waje.

Tsare-tsaren da Tinubu ya kawo

Kun ji labari ana zargin Gwamnatin Bola Tinubu ta dawo da tallafi ta bayan-fage, domin ainihin farashin man fetur ya zarce N1, 000.

Masana da wasu ‘yan kasuwa sun karyata kamfanin NNPCL, sun ce farashin fetur ya fi karfin N2, 500 a kasashen waje a kasuwar yau.

Kara karanta wannan

2024: Abubuwa 10 da Tinubu ya fadawa Najeriya a jawabin shiga sabuwar shekara

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng