Ganduje Ya Faɗi Matsala 1 Da Ke Neman Rusa Lissafin APC Gabanin Hukuncin Kotun Ƙolin Najeriya

Ganduje Ya Faɗi Matsala 1 Da Ke Neman Rusa Lissafin APC Gabanin Hukuncin Kotun Ƙolin Najeriya

  • Dakta Abdullahi Ganduje ya nuna rashin jin daɗinsa bisa yadda rikici ya ɓarke a jam'iyyar APC reshen jihar Benuwai
  • Shugaban APC na ƙasa ya buƙaci bangaren Gwamna Alia, shugabannin jam'iyya da ƴan majalisar na jihar su hakura su haɗa kansu
  • A cewarsa, jam'iyyar mai mulki ta kinkimo babban aiki na dawo da martabar Najeriya amma matsalar na neman rusa mata lissafi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya nuna damuwarsa kan rikicin cin gida da ya ɓarke a jam'iyyar reshen jihar Benuwai.

Ganduje, ya nuna rashin jin dadinsa game da rikicin da ya shiga tsakanin shugabannin APC na jihar, Gwamna Hyacinth Alia da kuma 'yan majalisar tarayya.

Kara karanta wannan

2024: Shugaba Tinubu ya bayyana babban buri ɗaya tal da ya sa ya nemi hawa mulki sau 3 a Najeriya

Shugaban APC na kasa, Abdullahi Ganduje.
Shugaban APC Ganduje Ya Nuna Damuwa Kan Rikicin Siyasar Jihar Benue Hoto: Official APC Nig
Asali: Twitter

Bisa haka ne Ganduje, tsohon gwamnan jihar Kano ya yi kira ga ɓangarorin uku su maida wuƙarsu kube, su haɗa kawunsu a samu zaman lafiya, Leadership ta tattaro.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ganduje ya yi wannan furucin ne yayin kaddamar da ginin sakateriyar APC da aka sabunta kuma aka raɗawa suna, 'Tinubu House' a Makurɗi, babban birnin jihar Benuwai ranar Laraba.

Muna bukatar zama tsintsiya ɗaya - Ganduje

Ya jaddada cewa hadin kai ne kadai hanyar da jam’iyyar za ta samu zaman lafiya kuma ta mai da hankali kan ci gaban jihar.

A rahoton Tribune, tsohon gwamnan ya ce:

"APC na aiki tukuru ƙarƙashin ajendar shugaban ƙasa, Bola Tinubu, domin dawo da martabar Najeriya, kuma zamu cimma nasara ne kaɗai idan mun dunƙule wuri ɗaya."
"Muna alfahari da jam'iyyar APC ta Benue saboda wannan ginin da ta mana, jihar nan tamkar gida take a wurin APC. Mun ɗan tafi hutu ne amma yanzu mun dawo da karfi, mulki na hannun mu."

Kara karanta wannan

Harin Plateau: Jam'iyyar PDP ta fadi laifin Tinubu, ta gaya masa muhimmin abu 1 da ya kamata ya yi

"Mun tsara yadda jam'iyya mai mulki zata cimma nasara shiyasa kuka ga kowane ofishin APC tun daga gunduma, kananan hukumomi jiha da na shiyya mun tsara yadda zasu tafiyar da ayyukansu."

Wannan kalamai na Ganduje na zuwa ne yayin da shari'ar zaben gwamnan Benuwai ta kai gaban kotun koli, wacce zata raba gardama tsakanin APC da PDP.

Hadimai sun fara aje aiki a Ondo

A wani rahoton kuma Rasuwar Gwamna Rotimi Akeredolu jiya Laraba ta kawo sabon sauyi a gwamnatin jihar Ondo kuma har an rantsar da sabon gwamna

Jim kaɗan bayan mutuwar Akeredolu, rahoto ya nuna akalla hadimai uku ne suka miƙa takardar murabus daga muƙamansu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262