Jerin Manyan Ƴan Siyasar Najeriya da Kotu Ta Yanke Wa Hukuncin Zaman Gidan Gyaran Hali a 2023

Jerin Manyan Ƴan Siyasar Najeriya da Kotu Ta Yanke Wa Hukuncin Zaman Gidan Gyaran Hali a 2023

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Kowane mutum yana son a masa adalci amma a wasu lokutan zaku ga ɗan siyasa a Najeriya ya tsinci kansa a gidan gyaran hali bisa wani laifi da ya aikata.

Duba da yadda cin hanci ya yi wa ƙasar nan katutu, karkatar kuɗin baitul mali da kesa-kesan bogi ba sabbin laifuka bane, sayen kuri'u da sauransu, ya kamata a ce kotu ta ɗaure ƴan siyasa fiye da yadda aka gani a 2023.

Yan siyasan da aka ɗaure a 2023.
Jerin Manyan Ƴan Siyasa da Kotu Ta Ɗaure a Gidan Yari a Shekarar 2023 Hoto: @iamekweremadu/Court of Appeal
Asali: UGC

Sai dai duk da waɗannan laifuka, ƴan siyasa suna da hanyar da suke kubuta daga irin waɗan shari'o'in ta hanyar amfani da lauyoyi manya da zasu kare su a kotu.

Legit Hausa ta tattaro muku manyan ƴan siyasa biyu da kotu ta sa suka girbi laifukan da suka shuka a shekarar 2023, ga su kamar haka:

Kara karanta wannan

Nazarin shekara: Shugaba Tinubu da wasu manya jigan-jigan siyasa da suka samu gagarumar nasara a 2023

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ike Ekweremadu

Mutum na farko da zai fara zuwa zuciyar ƴan Najeriya shi ne tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike Ekweremadu, wanda aka yi wa ɗaurin shekara tara da watanni takwas a Burtaniya.

Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, kotu ta yanke wannan hukukci a ranar 5 ga watan Mayu, 2023 bayan ta kama Ekweremadu da laifin safarar sassan jikin ɗan adam.

Kotun ta kama Ekweremadu, matarsa da likitansu, Obinna Obeta da laifin haɗa baki wajen ɗauko matashi ɗan shekara 21 daga Legas zuwa Landan domin cire masa ƙoda.

Sun kai matashin mai saye da siyarwa a kan titin Legas ƙasar Burtaniya ne da nufin cire masa koda ɗaya a sanya wa ɗiyar babban ɗan siyasan mai suna, Sonia.

Wahab Hammed

A ranar Alhamis, 7 ga watan Disamba, 2023 aka ɗaure shugaban jam'iyyar APC na ƙaramar hukumar Surulere ta jihar Legas, tsawon shekara ɗaya a gidan gyaran hali.

Kara karanta wannan

"An fara ruwan kuɗi" Gwamnatin Tinubu ta fitar da sabuwar sanarwa kan biyan kuɗin N-Power

Mai shari'a Isma'il Ijelu na babbar kotun jihar Legas mai zama a Ikeja, shi ne ya yanke wannan hukunci bayan kama Wahab da laifuka biyu na haɗa baki da cin hanci.

A cewar mai shigar da ƙara na hukumar yaƙi da rashawa EFCC, Samuel Daji, jigon APC ya haɗa kai da wani Segun Ijitola, suka riƙa siyan kuri'u a zaben shugaban ƙasa da na yan majalisar tarayya.

Amma mai shari'a Ijelu ya baiwa jigon APC mai mulki zaɓin biyan tara na Naira Miliyan ɗaya.

Tsohon gwamna ta tada hazo a PDP

A wani rahoton na daban kuma Kalaman tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamiɗo, kan rikicin jihar Ribas sun haddasa kace-nace a jam'iyyar PDP

Yayin da uwar jam'iyya ta ƙasa ta zargi Lamido da yi wa APC aiki, PDP ta Jigawa ta fito ta karyata ikirarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262