Kano: APC Ta Bukaci Kowa Ya Bi Yarjejeniyar Zaman Lafiya Da Aka Sa Hannu

Kano: APC Ta Bukaci Kowa Ya Bi Yarjejeniyar Zaman Lafiya Da Aka Sa Hannu

  • Jam'iyyar APC ta zargi wasu shugabannin NNPP da saɓawa yarjejeniyar zaman lafiyam da suka sa wa hannu a hedkwatar yan sanda
  • Mataimakin shugaban APC na Kano, Shehu Maigari, ya ce ya kamata 'yan sanda su ɗauki mataki domin a gabansu kowa ya sa hannu
  • Ya ce mambobin APC za su ci gaba da zama lafiya da harkokinsu na yau da kullum ba tare da tada zaune tsaye ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Mataimakin shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Kano, Shehu Maigari, ya bada tabbacin cewa za su ci gaba da bin yarjejeniyar zaman lafiya aka aka sa wa hannu a hukumar ‘yan sandan.

Kara karanta wannan

Ka jira ka ga makomarka tukunna, APC ta tura zazzafan gargadi ga Abba Kabir kan zargin abu 1 tak

Gawuna da Gwamna Abba Kabir.
Kano: APC Ta Bukaci Kowa Ya Bi Yarjejeniyar Zaman Lafiya da Aka Sa Hannu Hoto: Dr Nasir Gawuna, Abba Kabir Yusuf
Asali: Twitter

Maigari ya faɗi haka ne ranar Jumu'a yayin da yake amsa tambayoyin jaridar Leadership kan zanga-zangar da ƴan Kwankwasiyya ke yi.

Magoya bayan jam'iyyar NNPP mai kayan marmari na ci gaba da zanga-zanga domin nuna adawa da hukuncin kotun ɗaukaka ƙara na tsige Gwamna Abba Kabir Yusuf.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Da yake jawabi, mataimakin shugaban APC na Kano ya ce akwai zaman lafiya a jihar duba da yadda kowa ya maida hankali kan harkokinsa na yau da kullum.

APC ta zargi wasu da saɓa alkawarin zaman lafiya

Amma Maigari ya zargi wasu manyan mutane da saɓawa yarjejeniyar zaman lafiyar da aka rattabawa hannu ta hanyar fitowa zanga-zanga.

Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da kada su tsorata da abin da wasu ‘yan tsiraru suka aikata, su kwantar da hankalinsu su jira hukuncin kotun koli.

Kara karanta wannan

Farfesa Jega ya kawo hanyoyin da za a bi kafin a iya gyara hukumar INEC a Najeriya

Haka nan kuma ya roki hukumomin tsaro da ke kokarin tabbatar da bin doka da oda su tashi tsaye wajen tabbatar an bi yarjejeniyar kamar yadda kowa ya amince.

Shehu Maigari ya ce:

"Mutanen da ke Kano a halin yanzu sun san hakikanin halin da ake ciki, babu wani tashin hankali a jihar. Kowa yana gudanar da harkokinsa na yau da kullun."
“Babu tashin hankali a Kano a halin yanzu. Wasu mutane ne kawai masu son kai suke tsara abubuwan da ke faruwa mara daɗi."
"A makon jiya aka kira jam'iyyarmu APC da NNPP zuwa hedkwatar yan sanda muka sa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, amma abun ban mamakin mutanen nan sun saɓa."

Ya bayyana cewa yan sanda na wurin lokacin da kowace jam'iyya ta sanya hannu, don haka ya rataya a wuyansu su tabbatar an samu tsaro, Daily Post ta tattaro.

APC zata kwace wasu jihohi a kudu - Akpabio

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun rutsa manoma a gonakinsu, sun yi ajalin mutum biyu har lahira a jihar Taraba

A wani rahoton kuma Sanata Godswill Akpabio ya yi ikirarin cewa APC mai mulki zata karɓi jihohin Kudu maso Kudu a zabe na gaba.

Shugaban majalisar dattawan ya ce ya kamata shiyyar ta gode wa Shugaban Ƙasa Tinubu ta hanyar zaɓen jam'iyyar APC.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262