Labari Mai Zafi: SDP Ta Doke APC a Karamar Hukumar Farko da INEC ta Sanar a Kogi

Labari Mai Zafi: SDP Ta Doke APC a Karamar Hukumar Farko da INEC ta Sanar a Kogi

Kogi - Murtala Yakubu Ajaka wanda yake rike da tutar Social Democratic Party (SDP) ya shiga zaben jihar Kogi da kafar dama.

A sakamakon zaben farko da hukumar zabe na kasa watau INEC ta sanar, jam’iyyar SDP ce ta yi galaba a zaben Gwamnan Kogi.

Murtala Yakubu Ajaka ne ya fara samun nasara a kan Ahmad Usman Ododo da Dino Melaye a wajen takarar kujerar Gwamna.

Ga yadda sakamakon zaben ya fito kamar yadda labari ya iso mana inda ake da mutane 64,339 da aka yi wa rajista a 2023.

Daga ciki an tantance mutane 23, 044 da za su su kada kuri’a a zaben sabon Gwamnan.

Karamar hukumar Idu

APC: 2,033

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

PDP ta lshe karamar hukuma ta farko yayin da INEC ta fara tattara sakamakon karshe a Bayelsa

PDP: 271

SDP: 22,742

Rahotonmu ya nuna an yi watsi da kuri’u 280 daga cikin 23, 022 da aka kada a zaben.

Sai dai sakamakon zaben da su ke fitowa daga baya daga sauran kananan hukumomi sun nuna APC tana shan gaban SDP da PDP.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng