Zaben Gwamnan Bayelsa na 2023: Sakamako Zaɓe Daga Kananan Hukumomi Ya Fito, Kai Tsaye

Zaben Gwamnan Bayelsa na 2023: Sakamako Zaɓe Daga Kananan Hukumomi Ya Fito, Kai Tsaye

An gama zabe, ana tantance kuri'un kuma an fara kirgawa a wasu rumfunan zabe a jihar Bayelsa inda aka gudanar da zaben gwamna na 2023.

Kasance tare da mu domin samun bayanai kai tsaye dangane da tantancewa da kirga kuri'un da jami'an Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) ke yi kai tsaye.

An fara kidaya kuri'u a zaben gwamnan Bayelsa.
An kammala jefa kuri'u a wasu rumfunan zaben gwamnan Bayelsa na 2023 kuma an fara kidayan kuri'un. Hoto: Photo credits: Douye Diri, Engr Udengs Eradiri, Timipre Marlin Sylva
Asali: Facebook

Lura: Ku dinga sabunta shafin domin ganin sabbin bayanai.

Ijaw South LGA

APC - 18,174

LP - 119

PDP - 24,685

Masu zabe da suka yi rajista - 184,401

Kuri'u masu kyau - 43,158

Kuri'u marasa kyau - 663

Jimillar kuri'a da aka kada - 43,821

Karamar hukumar Brass

APC - 18,431

LP - 83

PDP - 12,602

Masu zabe da suka yi rajista - 94040

Masu zabe da aka tantance - 32064

An ɗage tattara sakamakon zaɓe sai zuwa Litinin

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta sanar da dage tattara sakamakon zaɓen gwammnan jihar Bayelsa, har sai zuwa ranar Litinin, 13 ga watan Nuwamba.

Premium Times ta ce hukumar ta ɗage tattara sakamakon zaɓen ne saboda ƙalubalen da ta fuskanta wajen tattara sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Brass da Southern Ijaw.

Ƙaramar hukumar Ekeremor

APC: 8,445

PDP: 23,172

LP: 50

Ƙaramar hukumar Nembe

Jam'iyyar APC ta samu nasara a ƙaramar hukumar Nembe.

APC: 22,248

PDP: 4,556

LP: 113

Ƙaramar hukumar Sagbama

APC: 6,608

PDP: 35,504

LP: 217

APC ta sake karban kaya a jihar Bayelsa

Timipre Sylva na jam'iyyar APC ya sha kaye a karamar hukumar Ogbia da ke jihar Bayelsa. Gwamna Douye Diri shi ya yi nasara a karamar hukumar da ratar kuri'u fiye da dubu biyu.

Ga yadda sakamakon zaben ya wakana. PDP: 18,435 APC: 16,319.

Karamar hukumar Yenagoa

APC - 14,534

LP - 244

PDP - 37,777

Karamar hukumar Ogbia

ADC - 56 ADP - 45

APC - 16,319 LP - 57 NRM - 37 NNPP - 4 PDP - 18,435

Gwamna Diri na PDP ya lashe ƙaramar hukumarsa

Sakamakon zaɓen karamar hukumar Kolokuma Opokuma.

APC - 5347

LP - 22

PDP - 18,465

NNPP - 22

ADC - 15

ADP -21

Jami'an tsaro sun taka wa masu zanga-zanga birki

Yayin da aka fara tattara sakamakon zaɓen Gwamnan jihar Bayelsa a cibiyar tattara sakamako ta INEC dake Yenagoa, an tsaurara matakan tsaro ta ko ina don aikin ya tafi cikin lumana.

Jami'an tsaro cikin shirin ko ta kwana, sun taka wa masu zanga-zanga na PDP birki, sun hana su shiga ofishin INEC da ke kan titin kasuwar Swali a babbam birni.

Daily Trust ta ce dakaru sun toshe titin da motocin sulƙe da na sintiri.

Sakamakon zaben Bayelsa

Rumfar zaɓe: Sambo I Open Space

Gunduma: Brass ta I

Karamar hukuma: Brass, Bayelsa

APC: 77

PDP: 168

NRM: 3

ZLP: 1

Rumfar zaɓe: Fire Station Open Space

Gunduma: Brass ta II

Ƙaramar hukuma: Brass, jihar Bayelsa

APC: 32

LP: 1

PDP: 72

APM: 1

Rumfar zaɓe: Twon Kubu Community Hall

Gunduma: Brass ta II

Ƙaramar hukuma: Brass, Bayelsa

APC: 72

PDP: 86

Rumfar zaɓe: Makarantar horar da malamai (NTI) Twon Brass

Gunduma: Brass ta II

Ƙaramar hukuma: Brass, Bayelsa

APC: 19

LP: 1

PDP: 29

PRP: 1

Rumfar zaɓe: Makarantar Firamare ta St. Barnabas, Twon

Gunduma: Brass Ward II

Ƙaramar hukuma: Brass, Bayelsa

APC: 19

PDP: 43

Bayelsa 2023: Gwamna Diri ya lashe rumfar zabensa

Akwatin zabe na Sampou/Kalama Ward, PU 004, Kolokuma/Opokuma LG, Bayelsa

APC - 0

ADP - 1

PDP - 218

LP - 0

Zaben gwamnan Bayelsa na 2023: Manyan yan takara

Ga wasu cikin manyan yan takara a zaben gwamnan jihar Bayelsa na 2023 da aka yi ranar Asabar 11 ga watan Nuwamba.

Alkalluman INEC sun nuna cewa yan takara da jam'iyyun siyasa 16 ne za su fafata a zaben. Sai dai, biyar din da aka jero kasa sune ake yi wa kallon manyan yan takara.

  • Douye Diri (PDP)
  • Timipre Sylva (APC)
  • Udengs Eradiri (Labour Party)
  • Waibodei Subiri (APGA)
  • Warmate Jones (Accord Party)

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164