Zaben Jihohi: Gagarumar Matsala Yayin da Aka Fara Siyan Kuri'u N15k, an Bayyana Mazabun

Zaben Jihohi: Gagarumar Matsala Yayin da Aka Fara Siyan Kuri'u N15k, an Bayyana Mazabun

  • Matsalar siyan kuri'u ita ke jefa al'umma cikin halin kakani-kayi yayin da ake gudanar da zabe
  • A jihar Bayelsa, a yau an samu matsalar siyan kuri'u wurin jama'a masu kada kuri'a a wasu mazabun jihar
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da kada kuri'a a jihohin Bayelsa da Kogi da kuma jihar Imo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Bayelsa - Yayin da ake ci gaba da kada kuri'a a jihar Bayelsa, an fara samun matsalar siyan kuri'u.

Ana zargin an fara siyan kuri'u kan makudan kudade inda mutane ke siyar da 'yancinsu a zaben.

'Yan siyasa sun fara biyan makudan kudade na siyan kuri'u
Zaben Jihohi: An fara siyan kuri'u a zaben jihar Bayelsa. Hoto: Timipre Sylva, Douye Diri.
Asali: Twitter

Mene mutane ke korafi a zaben?

TheCable ta tattaro cewa an jiyo wasu na maganan siyan kuri'u a wasu mazabu a birnin Yenagoa da ke jihar Bayelsa.

Kara karanta wannan

"15k daga APC, PDP na biyan 13k", Ana zargin siyan kuri'a a Bayelsa, Bayanai sun fito

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Masu zaben na fadin cewa ana siyan kuri'u a mazabar 017 a 'Ward' 10 na karamar hukumar Agudama-Ekpetiama da ke jihar.

Rahotanni sun tabbatar da cewa jam'iyyar APC na biyan naira dubu 15 yayin da PDP ke biyan dubu 13.

Wace matsala hakan ke jawo wa?

Siyan kuri'u na daga cikin manyan matsaloli da ke kawo cikas a dimukradiyya a Najeriya.

Matsalar siyan kuri'u na kawo cikas a zaben shugabanni nagari yayin da ake gudanar da zabe.

A babban zaben da aka gudanar a watan Faburairu da Maris, an samu irin wadannan matsaloli na siyan kuri'un jama'a.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.