Pdp Ta Gabatar Da Babban Bukata Bayan Batar Kayan Zabe a Hatsarin Jirgin Ruwan Bayelsa

Pdp Ta Gabatar Da Babban Bukata Bayan Batar Kayan Zabe a Hatsarin Jirgin Ruwan Bayelsa

Yenagoa, Jihar Bayelsa - Babban jam'iyyar hamayya a Najeriya, Peoples Democratic Party, PDP, ta bukaci a maye gurbin kayayyakin zabe da suka bace a hatsarin jirgin ruwa da ya faru a jihar Bayelsa.

Jam'iyyar ta PDP ta gabatar da wannan bukatar ne cikin wani gajeren sanarwa da ta fitar a ranar Asabar, 11 ga watan Nuwamba. An wallafa sanarwar a shafin jam'iyyar na kafar X.

PDP ta gabatar da muhimmin bukata ga INEC kan zaben Bayelsa
PDP ta bukaci INEC ta maye gurbin kayan zaben Bayelsa da duka salwanta a hatsarin jirgin ruwa. Hoto: @GovAgbuKefas
Asali: Twitter

"A kai kayan zabe Koluama": PDP ta fada wa INEC

Idan za a iya tunawa jami'an hukumar zabe 12 sun tsallake rijiya da baya lokacin da jirgin ruwa da ke dauke da su zuwa Koluama a karamar hukumar Kudancin Ijaw ya kife a daren ranar Juma'a, 10 ga watan Nuwamba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Zaben gwamnan Imo 2023: 'Yan sanda sun yi arangama da wakilan jam’iyya, an yi harbe-harbe

Takardun rubuta sakamakon zabe, na'urar caji, da jakunna dauke da kayan zabe da wasu kayayyakin jami'an na INEC duk sun salwanta.

A martaninta kan afkuwar lamarin, jam'iyyar PDP ta bukaci Hukumar Zabe mai Zaman Kanta (INEC) kada ta tauye wa mutanen yankin hakkinsu na yin zabe.

Sanarwar na PDP ya ce:

"Hukumar Zabe na Kasa mai Zaman Kanta (INEC) @inecnigeria ta tabbatar cewa ba a tauye wa mutanen Koluama da ke Karamar Hukumar Kudancin Ijaw na Jihar Bayelsa hakkin kada kuri'a a zaben gwamnan jihar Bayelsa ba saboda bacewar kayan zabe a ranar Juma'a, 10 ga watan Nuwamban 2023, a hatsarin jirgi.
"INEC ta tabbatar cewa an sake turawa mutanen kayan zabe a kan lokaci zuwa Koluama."

Kazalika, jam'iyyar ta ce "za ta cigaba da sa ido domin tabbatar da ingantaccen zabe a Jihar Bayelsa".

Dakaci karin bayani ...

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164