Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Sake Yanke Hukunci Kan Zaben Majalisar Tarayya, Ta Yi Bayani

Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Sake Yanke Hukunci Kan Zaben Majalisar Tarayya, Ta Yi Bayani

  • Kotun daukaka kara a yau Litinin ta yi hukunci kan shari'ar zaben Majalisar Tarayya a jihar Kano
  • Kotun ta tabbatar ma nasarar dan takarar jam'iyyar NNPP, Rabiu Yusuf Takai a matsayin wanda ya lashe zabe
  • Hassan Sani Tukur, hadimin gwamnan Kano a bangaren yada labarai na zamani shi ya bayyana haka a shafinsa na Twitter a yau Litinin

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Kotun daukaka kara ta yi hukunci kan shari'ar da ake a mazabar Tarayya ta Takai/Sumaila a jihar Kano.

Kotun wacce ta yanke hukunci a yau Litinin 6 ga watan Nuwamba ta tabbatar da nasarar Rabiu Yusuf Takai na jam'iyyar NNPP.

Kotun daukaka kara ta tabbatar da Yusuf Takai a matsayin dan Majalisar Tarayya a Kano
Kotu ta yi hukunci kan zaben Majalisar Tarayya a Kano. Hoto: @Noble_Hassan.
Asali: Twitter

Wane hukunci kotun ta yanke a Kano?

Kara karanta wannan

Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Yi Hukunci Kan Shari'ar Zaben Dan Majalisar Tarayya, Ta Fadi Mai Nasara

Hadimin Gwamna Abba Kabir na Kano a bangaren yada labarai ta zamani, Hassan Sani Tukur shi ya bayyana haka a shafin Twitter.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan na zuwa ne yayin da ake shirin fara sauraran shari'ar zaben gwamnan jihar Kano tsakanin Abba Kabir da Nasiru Gawuna.

Yayin hukuncin kotun zabe a watan Satumba, kotun ta tabbatar da Yusuf Takai a matsayin dan Majalisar Tarayya, tare da tarar naira dubu 20.

Hukunci a mazabar Kura/Madobi/Garun Malam

Wannan na zuwa ne awanni kadan bayan kotun daukaka kara ta yi hukunci kan shari'ar zaben Majalisar Tarayya a mazabar Kura/Madobi/Garun Malam.

Yayin hukuncin, kotun ta rusa zaben Musa Ilyasu Kwankwaso na jam'iyyar APC.

Ta kuma tabbatar da Yusuf Datti na jam'iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zabe.

Hukuncin na zuwa bayan korafe-korafen da dan takarar jam'iyyar NNPP, Datti ya shigar a gaban kotun bayan hukuncin kotun kararrakin zabe.

Kara karanta wannan

Kano: Bajiman lauyoyi sun yi watsa-watsa da hukuncin shari’ar Abba da Gawuna

Kotu ta tabbatar da nasarar Yusuf Datti a jihar Kano

A wani labarin, kotun daukaka kara ta yi hukunci kan shari'ar zaben Majalisar Tarayya da ke jihar Kano.

Kotun ta rusa nasarar Musa Ilyasu Kwankwaso na jam'iyyar APC a mazabar Kura/Madobi/Garun Malam da ke jihar.

Har ila yau, kotun ta tabbatar da Yusuf Datti na jam'iyyar NNPP a matsayin halastaccen wanda ya lashe zaben Majalisar Tarayya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.