Gwamnonin PDP Sun Yi Fatali da Tsagin Atiku, Sun Koma Bayan Shugaban Tinubu Kan Abu 1 Tak

Gwamnonin PDP Sun Yi Fatali da Tsagin Atiku, Sun Koma Bayan Shugaban Tinubu Kan Abu 1 Tak

  • Gwamnonin jam'iyyar PDP sun bayyana dalilinsu na mara wa shugaban ƙasa Tinubu baya kan rikicin siyasar jihar Ribas
  • A cewarsu, saɓanin tunanin masu sukar hakan wanda ke tare da Atiku, tsoma bakin Tinubu ya zama wajibi kuma dole a yaba masa
  • Wannan na zuwa ne yayin da Ministan Abuja ya ce ba ruwansa da harkokin mulkin Ribas amma zai kare tsarin siyasar da aka kafa a 2015

Ahmad Yusuf, gogaggen Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Gwamnonin jam'iyyar PDP sun jaddada goyon bayansu ga shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, kan yunkurinsa na shiga tsakani a rikicin siyasar jihar Ribas.

Gwamnonin PDP sun kare kansu kan goyon bayan Tinubu.
Rikicin Rivers: Dalilin da Ya Sa Muke Goyon Bayan Bola Tinubu, Gwamnonin PDP Hoto: thenation
Source: UGC

Sun bayyana cewa ƙungiyar gwamnonin Najeriya 36 (NGF) ta ƙagara ta ga an samu masalaha a rigimar wacce ta shiga tsakanin gwamna Similanayi Fubara da Nyesom Wike.

Kara karanta wannan

Wike Ya Zauna da ‘Yan Majalisa, Ya Jaddada Sharudan Sasantawa da Gwamnan Ribas

A cewarsu, tsoma baki da nufin sasanta rikicin wanda shugaban ƙasa ya kudiri aniya ya zama tilas domin guje wa yaɗuwar matsalar zuwa wasu jihohin, The Nation ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A nasa ɓangaren Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce ba shi da dalilin da zai sa ya yi katsalandan a harkokin mulkin Rivers, domin ya yi wa al’ummarta hidima na tsawon shekaru takwas.

Ya ci gaba da cewa babban abin da ya takaita a kai shi ne kare tsarin siyasar da aka gina tun shekarar 2015 a jihar Ribas.

Gwamnonin PDP sun jero dalilansu na goyon bayan Tinubu

Shugaban kungiyar Gwamnonin PDP kuma Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya kare tsoma bakin da Shugaba Tinubu ya yi a rikicin.

Saɓanin yadda wasu jiga-jigan da ke tare da Atiku Abubakar ke ikirarin cewa goyon bayan Tinubu na iya tarwatsa PDP, Bala ya ce yunƙurin ya yi daidai da ajendar NGF.

Darakta Janar na ƙungiyar gwamnonin PDP, CID Maduabum, shi ne ya faɗi haka a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce matakin da gwamnan Bauchi ya dauka abin alfahari ne.

Kara karanta wannan

A Ƙarshe, Gwamnan APC ya tona gaskiyar abinda ya sa Shugaban NLC na ƙasa ya ci dukan tsiya a Imo

Ya kara da cewa shiga taakanin da Tinubu ya yi a Ribas da rashin tsoma bakinsa a cikin shari’ar kotunan zabe abin yabawa ne, kamar yadda The Cable ta ruwaito.

Sanarwan ta ce:

"Dukkan gwamnonin jihohi 36 sun goyi bayan yunƙurin, musamman Shugaban ƙungiyar Gwamnonin PDP, Bala Mohammed, ya nuna goyon bayansa ga matakin Tinubu na shiga tsakani."

Kotu ta umurci a saki Emefiele

A wani labarin kuma Wata Kotu a babban birnin tarayya Abuja ta bada umarnin gaggauta sakin tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele.

Ta ce a sake shi ba tare da gindaya masa wasu sharuɗɗa ba, inda ta umarci EFCC da shugaban hukumar su aiwatar da wannan umarni.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262