Da Ɗumi-Ɗumi: "Ba Tinubu Ne Ya Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Ba" Atiku Abubakar Ya Yi Bayani
- Alhaji Atiku Abubakar ya nuna takaicinsa kan hukuncin da Kotun ƙolin Najeriya ta yanke a ƙarar da ya shigar makon da ya wuce
- Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana cewa duk da Kotun Allah ya isa ta yanke hukunci, tarihi zai wanke shi sarai
- Atiku ya faɗi haka ne a wurin taron manema labarai na duniya kan hukuncin Kotun, wanda ya gudanar ranar Litinin a Abuja
Ahmad Yusuf, Editan Legit Hausa ya shafe shekaru yana kawo rahotanni kan al'amuran siyasa da harkokin yau da kullum
FCT Abuja - Ɗan takarar shugaban ƙasa a inuwar PDP a zaben watan Fabrairu, 2023, Atiku Abubakar, ya jaddada matsayarsa cewa ba Bola Tinubu ya lashe zaɓe ba.
Atiku ya yi wannan furucin ne a sakateriyar PDP da ke Wadata Plaza, inda ya gudanar da taron manema labarai na duniya ranar Litinin. Legit Hausa ta bibiyi jawabin da ya yi.

Asali: Facebook
Daily Trust ta rahoto Atiku na cewa hukuncin da Alƙalan Kotun ƙoli suka yanke kan ƙarar da ya ɗaukaka ya nuna cewa, "komai ya lalace a ƙasar nan."
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jagoran 'yan adawan ɗan shekara 76 a duniya ya bayyana cewa matsalolin da Najeriya ke fama da su sun zarce zaɓen shugaban kasa kawai.
Ya ce ƙwararan shaidu sun nuna a zahiri cewa hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta karya dokar zaɓe wajen ayyana Tinubu a matsayin wanda ya samu nasara.
A kalamansa ya ce:
"Hukuncin da Kotun ƙoli ta yanke, duk da shi ne na ƙarshe ya nuna tabbas ba abin da ke tafiya daidai."
Meyasa Atiku ya yi rashin nasara a Kotu?
Idan baku manta ba, Kotun ƙolin Najeriya, ranar Alhamis da ta gabata, ta tabbatar da shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin sahihin wanda ya ci zaɓen shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan
Kotun Koli: Babban Malamin Addini Ya Yi Hasashen Abin da Zai Faru Bayan Yanke Hukunci
Jigon APC a Kudu maso Gabshin Najeriya, Okoye Francis, ya ce Atiku da Peter Obi sun yi rashin nasara a ƙarar da suka shigar saboda sun gaza gamsar da Kotu.
Ba zan gudu ba - Atiku
A wani rahoton kuma A karshe, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi martani kan hukuncin kotun koli.
Yayin ganawar da manema labarai wanda Legit ta bibibya, Atiku ya ce akwai tarun matsaloli a hukuncin da ta bai wa Bola Tinubu nasara a kotun koli.
Asali: Legit.ng