Malamin Addini Ya Magantu Kan Damar Peter Obi Na Zama Shugaban Kasa a 2027

Malamin Addini Ya Magantu Kan Damar Peter Obi Na Zama Shugaban Kasa a 2027

  • Primate Elijah Ayodele ya ce tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi, ba zai iya zama shugaban kasa ba a 2027
  • Primate Ayodele a ayyana cewa ba zai yi tasiri ba a siyasance a babban zaben Najeriya mai zuwa
  • Malamin addinin ya ce ana iya kallon gazawar Obi wajen lashe zaben shugaban kasa a 2023 a matsayin "alheri"

Jihar Lagos - Fitaccen malamin addini, Primate Babatunde Elijah Ayodele, ya yi watsi da damar Peter Obi na zama shugaban kasa a babban zabe mai zuwa a 2027.

Primate Ayodele ya ce da Obi, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar LP a zaben watan Fabrairun 2023, ya hade da Atiku Abubakar na PDP da bai fadi zaben ba.

Primate Ayodele ya ce Peter Obi ba zai yi tasiri ba a zaben 2027
Malamin Addini Ya Magantu Kan Damar Peter Obi Na Zama Shugaban Kasa a 2027 Hoto: Primate Babatunde Elijah Ayodele, Mr. Peter Obi
Asali: Facebook

"Obi ba zai iya zama shugaban kasa ba a 2027": Ayodele

Kara karanta wannan

'Yan Siyasa 5 Masu Neman Shugaban Kasa da Tinubu Ya Bai Wa Mukami a Gwamnatinsa

Kamar yadda malamin addinin ya bayyana, idan Obi ya yanke shawarar sake takara a zaben 2027, kawai 'bata kudinsa zai yi'.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Obi ba zai iya zama shugaban kasa a 2027 ba. Idan yana mafarkin haka, ya kamata ya manta kawai; magana ta gaskiya. Amma kana iya bata kudinka kuma. Ba kudina bane, kudinka ne.
"Za ka ga cewa ba za ka yi tasiri ba ko kadan a siyasance a 2027. Ba za su ganeka ba ko kadan. Duk wanda ke fada maka cewa ka dawo, haka za su dunga fada maka, 'yi wannan, yi wancan'.
"Wannan ya wuce. Dama ce ga Atiku da Obi, da sun hade. Za su lashe zaben (2023). Sannan kai (Obi) ba ka so jin gaskiya ba. Mun taya ka (Obi) murna kaima. Ba ka fadi ba, ka yi kokari sosai. Faduwa yana cikin alhairi."

Kara karanta wannan

Da Ɗumi-Ɗumi: Fitaccen Lauyan Najeriya Ya Yi Bayani Kan Nasarar da Tinubu Ya Samu a Kotun Ƙoli

Ganduje ya shawarci Atiku da Obi

A wani labari na daban, Shugaban APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya bukaci Atiku Abubakar da Peter Obi da su dauki na annabawa.

Ganduje ya shawarci manyan yan siyasar da su sake gwada sa’arsu a 2031. Lokacin zai yi daidai da kammala mulkin shugaban kasa Bola Tinubu na biyu.

Kotun koli dai ta tabbatar da nasarar Shugaban kasa Bola Tinubu a ranar Alhami,s 26 ga watan Oktoba inda ta yi fatali da kararrakin da sauran yan takarar shugaban kasa suka shigar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Online view pixel