Kotun Koli: Jam’iyyar LP Ta Taya Tinubu Murna, Ta Aika Sako Ga Atiku

Kotun Koli: Jam’iyyar LP Ta Taya Tinubu Murna, Ta Aika Sako Ga Atiku

  • Bangaren jam'iyyar LP da Lamidi Apapa ke jagoranta ta taya Shugaban kasa Bola Tinubu murn kan nasararsa a kotun koli
  • Abayomi Arabambi, kakakin bangeran, a cikin wata sanarwa da ya saki a ranar Asabar, ya ce nasarar da Tinubu ya samu ya cancanta
  • Arabambi ya kuma yi ba'a ga Peter Obi, yana mai cewa bai dauki alkalan kotun koli lokaci ba wajen yin fatali da karar da ya daukaka

FCT, Abuja - Bangaren jam'iyyar LP da Lamidi Apapa ke jagoranta ta taya shugaban kasa Bola Tinubu murnar nasarar da ya samu a kotun koli.

Kamar yadda jaridar Punch ta rahoto, bangaren LP din ta bukaci Shugaba Tinubu da ya zama mai karamci a nasara sannan ta nuna shirinta na shiga a dama da ita a sabuwar gwamnati.

Kara karanta wannan

Peter Obi Ya Shiga Yar Buya Bayan Ya Sha Kaye a Kotun Koli? Kakakin Kamfen Din LP Tanko Ya Magantu

Jam'iyyar LP ta taya Tinubu murnar nasara a kotun koli
Kotun Koli: Jam’iyyar LP Ta Taya Tinubu Murna, Ta Aika Sako Ga Atiku Hoto: Bola Ahmed Tinubu
Asali: Twitter

Bangaren LP ta yi ba'a ga Peter Obi kan kayen da ya sha a kotun koli

Haka kuma, bangaren jam'iyyar ta yi ba'a ga dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Peter Obi, tana mai cewa ko awanni bai dauki alkalan kotun koli ba wajen yin fatali da karar da ya daukaka.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ku tuna cewa a ranar Alhamis, 26 ga watan Oktoba, kotun koli ta yi fatali da kararrakin da Peter Obi da takwaransa na PDP, Atiku Abubakar suka daukaka a kan nasarar Shugaban kasa Bola Tinubu a zaben shugaban kasa na 2023.

Da yake martani ga hukuncin kotun koli a ranar Asabar, 28 ga watan Oktoba, Abayomi Arabambi, kakakin LP, ya ce Shugaba Tinubu ya cancanci nasarar da ya samu.

Bangaren LP ta bukaci Tinubu ya zama mai karamci cikin nasara

Kara karanta wannan

Albishir da Tinubu Ya Yi wa Hadimai Jim Kadan da ba Shi Nasara a Shari’ar Zaben 2023

"Yanzu nasara ta samu a n kawo karshen dukkan takkadamar da suka taso daga zaben shugaban kasa da na yan majalisar tarayya na ranar 25 ga watan Fabrairu. Muna fatan cewa shugaban kasar zai nuna karamci cikin nasara ta hanyar gayyatar shugabancin LP domin a hada hannu wajen ci gaban gwamnatinsa na hadin kan kasa baki daya.
"Yayin da mu a jam'iyyar LP muke rokon wadanda suka sha kaye, musamman dan takarar shugaban kasa na PDP, da su nuna kishin kasa a matsayin yan damokradiyya, muna bukatan wanda ya lashe zaben da ya nuna karamci cikin nasarfa tun da gwamnatin tamu ce mu dukka."

Shugaban LP ya kori hadimansa

A wani labarin, mun ji cewa hugaban jam’iyyar LP, Barista Julius Abure ya fatattaki wasu daga cikin hadimansa.

Abure ya dauki wannan matakin ne kwanaki biyu bayan jam’iyyar ta sha kaye a kotun koli da ta bai wa Tinubu nasara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Online view pixel