Sylva Ya Daukaka Kara Kan Hukuncin da Kotun da Ta Soke Takararsa a Zaben Bayelsa

Sylva Ya Daukaka Kara Kan Hukuncin da Kotun da Ta Soke Takararsa a Zaben Bayelsa

  • Ɗan takarar gwamna a inuwar APC a zaben jihar Bayelsa, Timipre Sylva, ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke
  • Tsohon ministan ya musanta hana shi takara da alkalin Kotun ya yi, ya roƙi Kotun daukaƙa ƙara ta tabbatar masa da takararsa
  • Kotun dai ta soke takarar Sylva na jam'iyyar APC bisa hujjar cewa sau biyu ana rantsar da shi a matsayin gwamnan Bayelsa

Bayelsa - Tsohon ƙaramin Ministan albarkatun man fetur, Timipre Sylva, ya ɗaukaka ƙara dangane da hukuncin da babbar Kotun tarayya mai zama a Abuja ta yanke.

The Nation ta tattaro cewa Sylva ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin wanda ya soke tikitin takararsa ta gwamna a inuwa jam'iyyar APC a zaben gwamnan jihar Bayelsa.

Tsohon minista, Timipre Sylva.
Sylva Ya Daukaka Kara Kan Hukuncin da Kotun da Ta Soke Takararsa a Zaben Bayelsa Hoto: Timipee Sylva
Asali: Twitter

Mai shari’a Okorowo, a hukuncin da ya yanke a yammacin ranar Litinin, ya kori Sylva bisa dalilin cewa an rantsar da shi sau biyu kuma ya yi mulki na tsawon shekaru biyar a matsayin gwamnan jihar Bayelsa.

Kara karanta wannan

Tsohon Jigon APC Ya Bukaci a Kori Tinubu Daga Shugabancin ECOWAS, Ya Bayyana Kwakkwaran Dalili

Tsohon ministan ya ɗaukaka ƙara

A takardar daukaka kara da aka shigar a ranar Talata, 10 ga watan Oktoba, Sylva ya yi fatali da hukuncin wanda mai shari’a Donatus Okorowo ya yanke kuma ya bukaci kotun da ta ajiye shi a gefe kana ta tabbatar masa da takara.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kuma shigar da buƙatar cewa a jingine aiwatar da hukuncin babbar Kotun tarayya har sai Kotun ɗaukaka ƙara ta yanke hukunci kan ƙarar da ya shigar.

Jam'iyyar APC ta yi fatali da hukuncin Kotun

A wata sanarwa da ta fitar ranar Talata, jam'iyyar APC reshen jihar Bayelsa ta ce ba ta yarda da hukuncin hana Sylva takara ba, inda ta sha alwashin ɗaukaka ƙara.

A cewar APC, baki ɗaya ƙarar da jam'iyyar PDP ta shigar a gaban Kotun ta saɓa wa kundin dokokin zaɓen Najeriya, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Da Ɗumi-Dumi: Babbar Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Batun Tsige Mataimakin Gwamnan APC

Zaben Kogi: Jigon APC Ya Yi Murabus, Ya Fice Daga Jam'iyyar Zuwa AA

A wani rahoton kuma Jam'iyyar APC ta rasa ɗaya daga cikin manyan jiga-jiganta a jihar Kogi yayin da zaɓen gwamna ke ƙara kusantowa a wata mai zuwa.

Ɗan siyasan ya bayyana cewa ya yanke shawarar koma wa jam'iyyar AA ne domin tabbatar da daidaito, gaskiya da adalci a kujerar gwamnan jihar Kogi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262