Minista Balarabe Ya Bayyana Dalilin Sumansa A Majalisa Yayin Tantance Shi A Yau

Minista Balarabe Ya Bayyana Dalilin Sumansa A Majalisa Yayin Tantance Shi A Yau

  • Minista Balarabe Abbas ya bayyana dalilin faduwarshi a majalisar Dattawa yayin da ake tantance shi a yau Laraba
  • Balarabe wanda shi ne ya maye gurbin El-Rufai daga jihar Kaduna ya suma ana tsaka da tantance shi a yau
  • Ya bayyana wa shugaban majalisar, Goswill Akpabio cewa ya shafe kwanaki uku ya na aiki ba tare da hutawa ba

FCT, Abuja – Sabon minista daga jihar Kaduna ya bayyana dalilin sumansa a majalisar Dattawa a yau yayin tantance shi a dakin majalisar.

Balarabe Lawal ya fadi kasa lokacin da ake tantance shi a yau Laraba 4 ga watan Oktoba a Abuja, Legit ta tattaro.

Minista ya bayyana dalilin suman da ya yi a majalisar Dattawa
Minista Balarabe ya yi martani bayan ya suma yayin tantance shi a majalisa. Hoto: @kc_journalist/ Nigerian Senate.
Asali: UGC

Meye ya jawo faduwar ministan a majalisar?

Faduwarshi ke da wuya, shagaban majalisar ya bukaci a kawo masa dauki inda ya farfaɗo bayan wani lokaci.

Kara karanta wannan

Yanzu Yanzu: Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Zababben Ministan Da Ya Yanke Jiki Ya Fadi Da Wasu 2

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Balarabe daga bisani ya shaidawa shugaban majalisar, Godswill Akpabio dalilin faduwar tashi lokacin da ake tantance shi.

Balarabe ya bayyana cewa gajiya ce da ya yi ta jawo masa wannan matsalar inda ya ce ya shafe kwanaki da dama ya na aiki ba tare da hutawa ba, Aminiya ta tattaro.

A jita Talata ne shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya mika karin sunayen ministoci majalisar Dattawa don tantancewa.

Bayan Balarabe ya gabatar da kanshi da tarihin rayuwarshi kawai sai ya fadi kasa wanda tuni aka kawo masa agajin gaggawa.

Wane mataki majalisar ta dauka bayan suman ministan?

Shugaban majalisar, ya bukaci masu daukar hoto da faifan bidiyo da su dakata da dauka.

Majalisar ta shiga wani zama na sirri yayin da ake kula da lafiyar ministan a bayan fage inda aka dauke shi a motar daukar marasa lafiya zuwa asibiti.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: An Bayyana Halin Da Wakilin Jihar Kaduna Yake Ciki Bayan Ya Kife a Wajen Tantance Ministoci

Balarabe shi ne wanda ya maye gurbin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai a matsayin wakilin daga jihar Kaduna a Arewacin kasar.

El-Rufai ya rasa wannan damar ce bayan majalisar ta ki tabbatar da shi saboda matsalar da ta shafi tsaro.

Sabon minista ya suma a gaban majalisa yayin tantancewa

A wani labarin, sabon minista daga jihar Kaduna, Balarabe Abbas Lawal ya suma a gaban majalisa yayin da ake tantance shi.

Balarabe shi ya maye gurbin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai bayan rasa wannan damar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.