Zaben Gwamnan Jihar Imo Na 2023: Primate Ayodele Ya Yi Hasashen Wanda Zai Yi Nasara

Zaben Gwamnan Jihar Imo Na 2023: Primate Ayodele Ya Yi Hasashen Wanda Zai Yi Nasara

  • Primate Elijah Ayodele, shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual ya yi hasashen yadda sakamakon zaben gwamnan jihar Imo zai kasance
  • Ya yi hasashen cewa Gwamna Hope Uzodimma na jam'iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki ne zai lashe zaben
  • Primate Ayodele ya ce APC ta shirya ma zaben fiye da sauran jam'iyyun adawa

Jihar Imo - Gabannin zaben gwamna mai zuwa a jihar Imo, shahararren malamin addini Primate Elijah Ayodele ya yi hasashe kan wanda zai lashe zaben.

Za a yi zaben gwamnan jihar Imo a ranar Asabar, 11 ga watan Nuwamba, kamar yadda hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ta tsara.

Primate Ayodele ya ce APC ce za ta lashe zaben gwamnan Imo
Zaben Gwamnan Jihar Imo Na 2023: Primate Ayodele Ya Yi Hasashen Wanda Zai Yi Nasara Hoto: Daily Post
Asali: UGC

Za a gwabza a zaben tsakanin manyan jam'iyyun siyasa uku wato Peoples Democratic Party (PDP), the Labour Party (LP) da All Progressives Congress (APC).

Kara karanta wannan

Ganduje Ya Ƙara Yi Wa Jam'iyyar PDP Babban Lahani a Jihar Arewa, Jigo Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

Da yake bayyana matsayinsa kan zaben mai zuwa, Primate Ayodele ya je shafinsa na soshiyal midiya a dandalin X, yana mai bayyana cewa ya hango APC a saman sauran jam'iyyun siyasa a zaben.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Ya rubuta:

"Na hango cewa zaben gwamna da ke tafe a jihar Imo nasara zai zama a bangaren jam'iyyar All Progressive Congress, domin a shirye suke sosai don samun nasara fiye da kowace jam'iyyar siyasa."

Zaben Imo: Dalilin da yasa Uzodimma na APC zai yi nasara - Primate Ayodele

A wani bidiyo da ya biyo rubutun nasa, ya bayyana cewa APC ta fi shirya ma zaben foye da yan adawa.

Ya ce APC ba za ta yi nasara ba idan gwamna mai ci Hope Uzodimma, ya gaji da kujerar shugabancin.

A halin da ake ciki, Gwamna Uzodimma zai kara da Sanata Samuel Anyanwu na jam'iyyar PDP da Cif Ukaegbu Ikechukwu Joseph na jam'iyyar Labour Party.

Kara karanta wannan

Jerin Ministocin Tinubu Da Kotun Zabe Ta Ayyana a Matsayin Wadanda Suka Lashe Zaben Yan Majalisun Tarayya

Gwamnan Akwa Ibom ya sanya dokar kulle a wasu kauyuka 4 na jihar

A wani labarin kuma, Gwamna Bassey Otu na jihar Cross Rivers a ranar Talata ya sanya dokar kulle a ƙauyukan Ugaga, Igbekurekor, Benekaba da Ijama na ƙaramar hukumar Yala ta jihar.

Gwamnan ya sanya dokar kullen ne bayan an samu ɓarkewar rikici a ƙauyukan, cewar rahoton PM News.

Rikicin filaye da iyakoki a tsakanin ƙauyukan guda huɗu ya jawo matsalar rashin tsaro a yankin wacce ta haifar da asarar rayuka da dukiyoyi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng