Tinubu Zai Rantsar Da Sabbin Ministocin Gwamnatinsa a Fadar Shugaban Kasa: Kai Tsaye

Tinubu Zai Rantsar Da Sabbin Ministocin Gwamnatinsa a Fadar Shugaban Kasa: Kai Tsaye

A yau Litinin 21 ga watan Agustan 2023 ne ake sa ran Shugaba Bola Tinubu zai rantsar da sabbin ministocin gwamnatinsa a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, Dr George Akume, ya tabbatar da hakan a cikin sanarwa da ya fitar a daren ranar Laraba, 16 ga watan Agusta.

A cikin sanarwar da aka fitar da hannun Willie Bassey, shugaban sashin watsa labarai na ofishin SGF, an rahoto cewa ana sa ran wadanda za a rantsar za su taho da mutane da biyu kowannensu.

Wadanda za a rantsar da bakinsu ana fatan su isa fadar shugaban kasa misalin karfe 9 na safiyar ranar Litinin.

Ku kasance da Legit.ng Hausa don samun bayanai kai tsaye dangane da rantsar da ministocin na Tinubu.

Hotuna da bidiyon sababbin Ministoci

Mai taimakawa shugaban Najeriya a kafofin zamani, ya fitar da hotuna da bidiyo bayan rantsar da ministocin.

Bayan tsohon Gwamnan Ribas, Nyesom Wike ya zama Minista, an gan shi ya na gaisawa da Shugaba Bola Tinubu.

An san ma'aikatar kowane Minista

Tsohon hadimin shugaban kasa, Tolu Ogunlesi ya ce wannan ne karo farko da wadanda ake rantsarwa za su san ma’aikatun da za su rike.

Hakan ya sabawa al’adar da aka gani a lokacin Ummaru Yar’adua, Goodluck Jonathan da Muhammadu Buhari tsakanin 2007 da 2023.

An rantsar da Ministoci

Aminiya ta ce Lateef Fagbemi ya nacikin wadanda aka fara rantsarwa a kujerar minister, shi ya zama babban lauyan gwamnatin tarayya.

A sahun farkon akwai matan da su ka samu shiga cikin gwamnatin Bola Tinubu irinsu Ekperipe Ekpo, Nkiruka Onyejeocha da Uju Kennedy.

Haka zalika an rantar da ministan ilmi, Farfesa Tahir Maman SAN da farko-farko.

Bayan nan sai aka rantsar da Sanata Abubakar Kyari a matsayin Ministan Noma da kuma Yusuf M. Tuggar da Ali Pate duka daga jihar Bauchi.

Farfesa Joseph Utsev da Sanata Heineken Lokpobiri sun yi rantsuwa a Aso Rock.

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Online view pixel