Shugabannin APC Da Dama Sun Yi Murabus Daga Kujerunsu a Jihar Neja

Shugabannin APC Da Dama Sun Yi Murabus Daga Kujerunsu a Jihar Neja

  • Yan kwanaki bayan murabus din shugaban APC a jihar Neja, wasu karin jami'an jam'iyya mai mulki sun sauka daga kujerunsu
  • A baya-bayan nan, Sakataren jam'iyyar, Barista Khaleel Ibrahim Aliyu da mataimakin shugaban jam'iyyar, Abdulsalam Madaki sun ajiye mukaminsu
  • Jam'iyyar APC ta jaddada cewar babu wani rikicin cikin gida da ya dabaibayeta kamar yadda ake hasashe

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Niger - Yan kwanaki bayan shugaban jam'iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Neja, Haliru Zakari Jikantoro, ya yi murabus daga kujerarsa, wasu karin mutum biyu sun ajiye mukamansu a jam'iyyar mai mulki.

Sakataren jam'iyyar, Barista Khaleel Ibrahim Aliyu da mataimakin shugaban jam'iyyar, Abdulsalam Madaki sun yi murabus.

Logon jam'iyyar APC mai alamar tsintsiya
Shugabannin APC Da Dama Sun Yi Murabus Daga Kujerunsu a Jihar Neja Hoto: Premium Times
Asali: UGC

Dalilin su na sauka daga mukamansu

Sai dai sun bayyana cewa matakin da suka dauka bai da alaka da rikicin da ya kunno kai a jam'iyyar tun bayan zabar Mohammed Idris Malagi a matsayin minista, jaridar Daily Trust ta rahoto.

Kara karanta wannan

Kano: "APC Za Ta Fatattaki Abba Gida Da Sauransu a Kotu", Abdullahi Abbas

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Amma wasu 'ya'yan jam'iyyar sun ce murabus din da suka yi umurni ne daga sama domin gwamnan bai aminta da shugabancin jam'iyyar a jihar ba tun bayan zaben fidda gwanin gwamna na 2022.

Karin jami'an APC za su yi murabus, majiyoyi

Majiyoyi sun ce akwai karin jami'an APC da za su yi murabus a kwanaki masu zuwa domin ba masu biyayya ga gwamnan damar jan ragamar harkokin jam'iyyar a jihar.

Da aka tuntube shi, sakataren labarai na jam'iyyar, Musa D. Sarkinkaji, ya fada ma Daily Trust cewa jam'iyyar bata fuskantar rikicin cikin gida kamar yadda mutane ke hasashe.

Ya ce jami'an jam'iyyar uku sun yi murabus ne da kansu domin gudanar da wasu harkokin.

Shugaban APC a jihar Neja ya yi murabus daga kujerarsa

A baya Legit.ng ta rahoto cewa shugaban jam'iyyar APC a jihar Neja, Haliru Zakari Jikantoro, ya yi murabus daga kan kujerarsa.

Kara karanta wannan

WAIWAYE: ‘Na Fi So Na Ba Tinubu Gudunmawa Daga Waje’, El-Rufai Ya Magantu Kan Mukamin Minista

Kamar yadda rahotanni suka kawo, Jikantoro ya yanke shawarar sauka daga mukaminsa ne a bainar jama'a ba tare da bayyana wani dalili ba.

Hakan na zuwa ne bayan wata ganawa da kwamitin aiki na jam'iyyar a jihar suka yi a sakatariyar APC da ke garin Minna, a gaban babban mai ba gwamnan jihar shawara kan harkokin siyasa, Alhaji Mohammed Nma Kolo.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng